• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Ake Zakkar Shan Ruwa Da Sallar Idi

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
2 years ago
in Dausayin Musulunci
0
Yadda Ake Zakkar Shan Ruwa Da Sallar Idi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ganin cewa Azumin Ramadan na bana ya kai karshe, a yau darashin namu zai yi bayani ne a kan Zakatul Fidir. Ma’anarta ita ce Zakkar Shan Ruwa, ita ce da Hausa wasu ke ce ma ta Zakkar Fid da Kai.

Zakkar wajiba ce a kan kowane Musulmi, yaro ko babba, namiji ko mace, da ko bawa. Ta wajaba a kan mutum da wadanda suke karkashinsa, wato wadanda ciyar da su yake kansa. Matansa da ‘ya’yansa da masu yi masa hidima wadanda yake rike da su yake ciyar da su.

  • Da Dumi-Dumi: Sarkin Musulmi Ya Ayyana Juma’a A Matsayin Ranar Sallah
  • Bunkasuwar Kasar Sin Mai Inganci Ta Ingiza Kwarewar Jama’arta

Bayar da zakkar ta zama wajibi ga duk Musulmin da ya mallaki abincin da zai ci shi da iyalansa na kwana da yini kuma koda mudu daya na hatsi ya ragu masa. Abin da ake nufi shi ne, idan mutum yana da abincin da zai ishe shi ci tare da iyalansa, bayan ya ware wannan sai ya kasance an samu ragowar mudu daya, Zakkar ta hau kansa. Amma wanda ba shi da shi ta fadi a kansa, sai dai idan ya samu ya bayar, ta zama kamar bashi kenan.

Amfanin Bayar Da Zakkar

Amfanin bayar da Zakkar shi ne domin mutum ya tsarkake kansa daga suratai marasa amfani ko batsar da ya aikata a cikin watan Azumin Ramadan domin ibadar da ya yi ta Azumi ta kubuta lafiya kalau. Haka nan amfaninta ya hada da ciyar da talakawa da almajirai wadanda ba su da abincin da za su ci don yaye masu kunci na rashin abincin, domin kuma kar a gan su sun fito suna bara.

Labarai Masu Nasaba

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

An farlanta Zakkar ta Shan Ruwa ce a watan Sha’aban, bayan Hijirar Annabi (SAW) da shekara biyu.

Yadda Ake Ba Da Ita

Ana ba da ita kafin a fita zuwa Sallar Idi ko kafin Ranar Sallah da kwana daya ko biyu. Abin da ake bayarwa shi ne Muddan Nabiyy (mudun awo ne dan madaidaici wanda za a iya auna shi da cikin tafukan hannun mutum mai matsakaicin tsawo) guda hudu a kan kowane mutum. Ana fitarwa daga dukkan nau’in abinci, kamar mu a nan mu ce shinkafa, masara, doya, dawa, dauro, cukwi, nono da duk dai abin da galibin mutane suke amfani da shi a matsayin abinci.

Malaman Kasar Maroko wadda kasa ce ta Malaman Musulunci kuma ‘yan’uwanmu ne Malikawa; sun yi fatawa cewa ya halasta a ba da kudi a madadin abinci a Zakkar. Za a kimanta kudin adadin Muddan Nabiyy hudu da za a fitar sai a ba da. Wannan ya halasta.

Idan mutum ya yi nazarin hikimar ba da Zakkar, wato wadata talakawa da miskinai don kar a gan su suna bara saboda rashin abincin da za su ci a Ranar Sallah, wannan kudin da za a ba su sai ya fi musu dadi a kan tsabar abincin. Domin wani idan ka bashi hatsin watakila ba zai iya nikowa ba, toh ka ga shi a wurinsa kudin zai fi masa amfani fiye da dawa ko masara. Dan dama-dama shinkafa ko doya wanda duk za a iya dafawa ba sai an nika ba. Amma fa a lura, kowane irin abinci mutum ya bayar ya yi. Saboda amfanin kudin ne ya sa muka kawo wadannan bayanan.

An fi so a ba da Zakkar ga mutanen kirki daga cikin talakawa ko wadanda suke da almajirai a hannunsu wadanda idan an ba su ba za su je bara ba a ranar. Ita Shari’a ba ta so a ga kaskancin mutum a wannan ranar, so ake kowa ya nuna girman Musulunci, kodayake wasu ‘yan’uwa ba za su yarda ba, duk abin da aka ba su ba za su iya hakura ba sai sun fita bara. Toh amma kuma kar wannan ya sa a ce ba za a ba su ba.

Idan mutum ya fitar da Zakkar sai ya kasance babu miskinai a kusa da shi da zai ba su, to ya dauka ya kai wurin da suke ya ba su, kar ya ce ai tunda babu miskinai a kusa da shi shikenan ba sai ya ba da ba.

Fa’ida: hatta kafirin da ake zaune da shi in talaka ne za a iya ba shi Zakkar don ya wadata a wannan ranar. So ake Dan Adam ya zama ya wadata saboda albarkar ranar ta Sallah.

Sallar Idi

Sallar Idin Shan Ruwa (Karamar Sallah) da Sallar Idin Layya (Babbar Sallah kamar yadda galibin Hausawa ke cewa), an shar’anta su a Musulunci a shekarar farko da yin Hijirar Annabi (SAW) daga Makka zuwa Madina. Kuma Annabi (SAW) ya dauwama a kansu (yana aikatawa). Ya hori maza da mata da yara da manya su fita zuwa gare su, ma’ana su je Masallacin Idi.

Ana so a yi wanka, a sa turare, a sanya mafi kyan tufafi da mutum yake da shi. A Sallar Idin Shan Ruwa, ana so a ci abinci kafin a fita zuwa Masallaci koda dabino ne ko shayi. Ana so a dan jinkirta ta kadan; sabanin Sallar Idin Layya da aka fi so a jinkirta cin abinci har sai an dawo. Idan mutum ya samu ikon yin Layya; ana so ya bude baki da naman Layyar sannan an fi so a gaggauta yin ta domin a dawo gida a yi Layya.

Ba a yin Sallar Idi (duka biyun) a Rufaffen Masallaci sai dai in akwai lalura kamar ta ruwan sama. A wajen gari ake fita yin SallarIdodin biyu ko kuma duk filin da aka samu. Annabi (SAW) bai taba yin Sallar Idi a Rufaffen Masallaci ba sai sau daya saboda ruwan sama kamar yadda Hakim ya ruwaito Hadisin.

Ana so a canja hanyar da aka je Masallacin Idi wajen dawowa amma ba dole ba ne. Ana so a yi Sallar Idin Shan Ruwa kamar da misalin karfe bakwai da rabi na safe (7:30am), Sallar Layya kuma kamar da misalin karfe bakwai na safe (7:00am). Amma ko sun kai karfe goma sha daya na rana babu laifi, duk lokacin yin su ne.

Ba a yin Kiran Sallah ko Ikamah ko cewa “a tashi a yi sallah”. Da zaran Sarki ko wanda ya tsaya a matsayinsa ya iso filin masallaci sai a mike a shiga Sallah. A raka’ar farko; bayan Kabbarar Harama sai a kara Kabbara shida, sun zama bakwai kenan. A raka’a ta biyu; bayan Kabbarar Tasowa daga Sujuda sai a kara Kabbara biyar, sun zama shida kenan. Ba a yin Nafila kafin Sallar Idi (duka biyu) kuma ba a yi a bayanta. Liman zai yi huduba bayan an yi sallama, wanda yake so zai zauna ya ji wanda wani uzuri ya kama shi sai ya tashi ya tafi ba tare da ya yi magana (surutai) ba.

Ana so a yi wasanni, da kade-kade, da wake-wake, da ciye-ciye, da nishadi, da ziyarori, da yi wa juna murnar Idi. Ana so a yi kallon wasannin ko rawar da ake yi, duk ya halatta a wannan ranar. Wannan shi ne Musulunci sassauka kamar yadda Annabi (SAW) ya fada, Tirmizhi da Ibn Majah da Baihaki suka fitar.

Allah ya sa mu kammala Azumi lafiya, mu yi Sallah lafiya, ya hore wa dukkan Musulmi abin da za a yi hidimomin Sallah da shi, Allah ya karba mana ibadunmu kuma ya karbe mu da falalarsa albarkar Annabi (SAW).

Wa sallallahu alal fatihil khatimil hadi wa ala alihi hakka kadrihi wa mikdarihil aziym.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HatsiSallar IdiZakkaZakkar Fidda Kai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bikin Sallah: Dauda Lawal Ya Taya Musulmi Murna, Ya Nemi A Dage Da Addu’a

Next Post

Karamar Sallah: Buhari, Tinubu, Atiku, Lawan, Gbajabiamila Sun Bukaci Zaman Lafiya

Related

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa
Dausayin Musulunci

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

2 weeks ago
Ramadan
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

3 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

4 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

1 month ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)

1 month ago
Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah
Dausayin Musulunci

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

2 months ago
Next Post
Karamar Sallah: Buhari, Tinubu, Atiku, Lawan, Gbajabiamila Sun Bukaci Zaman Lafiya

Karamar Sallah: Buhari, Tinubu, Atiku, Lawan, Gbajabiamila Sun Bukaci Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.