• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Amurka Ke Kwaton Albarkatun Kasa Da Kasa Da Sunan Yaki Da Ta’addanci

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Amurka Ke Kwaton Albarkatun Kasa Da Kasa Da Sunan Yaki Da Ta’addanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An kara ba da rahoton yadda Amurka ta saci albarkatun Syria. An ce, a farkon wannan watan da muke ciki, sojojin Amurka da ke Syria sun yi jigilar tarin bawon alkama da suka sata daga arewa maso gabashin Syria zuwa sansaninsu da ke arewacin kasar Iraki. Ba a jima ba, sojojin sun kara yin jigilar mai da suka sata daga gonakin mai dake arewa maso gabashin kasar. Kididdigar da aka yi ta shaida cewa, cikin makon da ya gabata ne, sojojin Amurka suka saci mai da yawansa ya kai a kalla daruruwan ton daga Syria. 

Hasali ma dai, tun bayan da Amurka ta jibge sojojinta a kasar ta Syria a shekarar 2015 bisa sunan wai “yaki da ta’addanci”, ba ta ko taba daina wawushe albarkatun kasar ba. Har ma don samun saukin aikin, ta girke sojojin kasar musamman a yankunan da aka fi noman hatsi da ma hakar mai a kasar. Alkaluman da gwamnatin Syria ta samar sun shaida cewa, sama da kaso 80% na mai da aka samar a kasar a farkon rabin shekarar 2022, sojojin Amurka ne da ma dakarun da suke wa goyon baya suka sace.

  • Shugaban Syria Ya Jinjinawa Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Yanzu haka, kimanin kashi 90% na al’ummar kasar Syria na cikin kangin talauci, kuma kashi 2/3 nasu na dogara ga gudummawar jin kai da aka samar musu, baya ga sama da rabinsu ba su iya samun isassun abinci. Duk da haka, Amurka wadda kullum ke yi wa kanta ikirarin “mai fafutukar kare hakkin dan Adam”, ba ta daina sace albarkatun al’ummar kasar Syria ba, har ma ba ta ko boye laifin da ta aikata ba, ganin yadda tsohon shugaban kasar ta Amurka Donald Trump ya amince a fili cewa, dalilin kasancewar sojojin Amurka a Syria shi ne don kwace mai na kasar. Mataimakiyar shugaban kasar ta Amurka Kamala Harris ma ta bayyana cewa, “cikin dimbin shekarun baya, Amurkawa sun yi ta yin fada ne don albarkatun mai.”

Lallai maganar madam Harris ta tono mana sirrin yakin da kasarta ta tayar da sunan yakar ta’addanci a kasashe da dama, ciki har da Afghanistan da Iraki da Syria da sauransu. Abin da a bakinta ta ce wai “yaki da ta’addanci”, a hakika abu ne da zai taimaka ga bauta wa moriyar kasar ne kawai.

Da zaran Amurka ta ga albarkatun da take so a wata kasa, to, samar da dalili ne kawai ya rage ta yi don kwace su. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

Labarai Masu Nasaba

Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinSyria
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rufe Boda: Mukaddashiyar Shugabar NIS Ta Ziyarci Iyakar Nijeriya Da Nijar Da Ke Illela

Next Post

Ganduje Ya Nada Tsohon Kwamishinansa Garba, Shugaban Ma’aikatan Jam’iyyar APC 

Related

Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani
Daga Birnin Sin

Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

1 hour ago
Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

4 hours ago
Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
Daga Birnin Sin

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

20 hours ago
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

22 hours ago
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
Daga Birnin Sin

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

23 hours ago
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

1 day ago
Next Post
Ganduje Ya Nada Tsohon Kwamishinansa Garba, Shugaban Ma’aikatan Jam’iyyar APC 

Ganduje Ya Nada Tsohon Kwamishinansa Garba, Shugaban Ma’aikatan Jam'iyyar APC 

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno

June 25, 2025
Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

Shawarar Gudanar Da Harkokin AI Na Duniya Na Jagorantar Ci Gaban Wayewar Kan Dan Adam Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani

June 25, 2025
Sojoji

DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS

June 25, 2025
Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO

June 25, 2025
Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 

June 25, 2025
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

June 25, 2025
Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

June 25, 2025
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

June 25, 2025
KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano

June 25, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Kashe Ɗan Kasuwa da Ɗan Banga A Kwara

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.