• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Amurka Ke Kwaton Albarkatun Kasa Da Kasa Da Sunan Yaki Da Ta’addanci

byCMG Hausa
2 years ago
Amurka

An kara ba da rahoton yadda Amurka ta saci albarkatun Syria. An ce, a farkon wannan watan da muke ciki, sojojin Amurka da ke Syria sun yi jigilar tarin bawon alkama da suka sata daga arewa maso gabashin Syria zuwa sansaninsu da ke arewacin kasar Iraki. Ba a jima ba, sojojin sun kara yin jigilar mai da suka sata daga gonakin mai dake arewa maso gabashin kasar. Kididdigar da aka yi ta shaida cewa, cikin makon da ya gabata ne, sojojin Amurka suka saci mai da yawansa ya kai a kalla daruruwan ton daga Syria. 

Hasali ma dai, tun bayan da Amurka ta jibge sojojinta a kasar ta Syria a shekarar 2015 bisa sunan wai “yaki da ta’addanci”, ba ta ko taba daina wawushe albarkatun kasar ba. Har ma don samun saukin aikin, ta girke sojojin kasar musamman a yankunan da aka fi noman hatsi da ma hakar mai a kasar. Alkaluman da gwamnatin Syria ta samar sun shaida cewa, sama da kaso 80% na mai da aka samar a kasar a farkon rabin shekarar 2022, sojojin Amurka ne da ma dakarun da suke wa goyon baya suka sace.

  • Shugaban Syria Ya Jinjinawa Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Yanzu haka, kimanin kashi 90% na al’ummar kasar Syria na cikin kangin talauci, kuma kashi 2/3 nasu na dogara ga gudummawar jin kai da aka samar musu, baya ga sama da rabinsu ba su iya samun isassun abinci. Duk da haka, Amurka wadda kullum ke yi wa kanta ikirarin “mai fafutukar kare hakkin dan Adam”, ba ta daina sace albarkatun al’ummar kasar Syria ba, har ma ba ta ko boye laifin da ta aikata ba, ganin yadda tsohon shugaban kasar ta Amurka Donald Trump ya amince a fili cewa, dalilin kasancewar sojojin Amurka a Syria shi ne don kwace mai na kasar. Mataimakiyar shugaban kasar ta Amurka Kamala Harris ma ta bayyana cewa, “cikin dimbin shekarun baya, Amurkawa sun yi ta yin fada ne don albarkatun mai.”

Lallai maganar madam Harris ta tono mana sirrin yakin da kasarta ta tayar da sunan yakar ta’addanci a kasashe da dama, ciki har da Afghanistan da Iraki da Syria da sauransu. Abin da a bakinta ta ce wai “yaki da ta’addanci”, a hakika abu ne da zai taimaka ga bauta wa moriyar kasar ne kawai.

Da zaran Amurka ta ga albarkatun da take so a wata kasa, to, samar da dalili ne kawai ya rage ta yi don kwace su. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Ganduje Ya Nada Tsohon Kwamishinansa Garba, Shugaban Ma’aikatan Jam’iyyar APC 

Ganduje Ya Nada Tsohon Kwamishinansa Garba, Shugaban Ma’aikatan Jam'iyyar APC 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version