ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Amurka Ke Kwaton Albarkatun Kasa Da Kasa Da Sunan Yaki Da Ta’addanci

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

An kara ba da rahoton yadda Amurka ta saci albarkatun Syria. An ce, a farkon wannan watan da muke ciki, sojojin Amurka da ke Syria sun yi jigilar tarin bawon alkama da suka sata daga arewa maso gabashin Syria zuwa sansaninsu da ke arewacin kasar Iraki. Ba a jima ba, sojojin sun kara yin jigilar mai da suka sata daga gonakin mai dake arewa maso gabashin kasar. Kididdigar da aka yi ta shaida cewa, cikin makon da ya gabata ne, sojojin Amurka suka saci mai da yawansa ya kai a kalla daruruwan ton daga Syria. 

Hasali ma dai, tun bayan da Amurka ta jibge sojojinta a kasar ta Syria a shekarar 2015 bisa sunan wai “yaki da ta’addanci”, ba ta ko taba daina wawushe albarkatun kasar ba. Har ma don samun saukin aikin, ta girke sojojin kasar musamman a yankunan da aka fi noman hatsi da ma hakar mai a kasar. Alkaluman da gwamnatin Syria ta samar sun shaida cewa, sama da kaso 80% na mai da aka samar a kasar a farkon rabin shekarar 2022, sojojin Amurka ne da ma dakarun da suke wa goyon baya suka sace.

  • Shugaban Syria Ya Jinjinawa Rawar Da Kasar Sin Ke Takawa Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Yanzu haka, kimanin kashi 90% na al’ummar kasar Syria na cikin kangin talauci, kuma kashi 2/3 nasu na dogara ga gudummawar jin kai da aka samar musu, baya ga sama da rabinsu ba su iya samun isassun abinci. Duk da haka, Amurka wadda kullum ke yi wa kanta ikirarin “mai fafutukar kare hakkin dan Adam”, ba ta daina sace albarkatun al’ummar kasar Syria ba, har ma ba ta ko boye laifin da ta aikata ba, ganin yadda tsohon shugaban kasar ta Amurka Donald Trump ya amince a fili cewa, dalilin kasancewar sojojin Amurka a Syria shi ne don kwace mai na kasar. Mataimakiyar shugaban kasar ta Amurka Kamala Harris ma ta bayyana cewa, “cikin dimbin shekarun baya, Amurkawa sun yi ta yin fada ne don albarkatun mai.”

ADVERTISEMENT

Lallai maganar madam Harris ta tono mana sirrin yakin da kasarta ta tayar da sunan yakar ta’addanci a kasashe da dama, ciki har da Afghanistan da Iraki da Syria da sauransu. Abin da a bakinta ta ce wai “yaki da ta’addanci”, a hakika abu ne da zai taimaka ga bauta wa moriyar kasar ne kawai.

Da zaran Amurka ta ga albarkatun da take so a wata kasa, to, samar da dalili ne kawai ya rage ta yi don kwace su. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

 

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Next Post
Ganduje Ya Nada Tsohon Kwamishinansa Garba, Shugaban Ma’aikatan Jam’iyyar APC 

Ganduje Ya Nada Tsohon Kwamishinansa Garba, Shugaban Ma’aikatan Jam'iyyar APC 

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.