• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bikin Yara Na Duniya Ya Gudana A Kebbi

by Umar Faruk
9 months ago
in Labarai
0
Yadda Bikin Yara Na Duniya Ya Gudana A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kebbi da Asusun Tallafa wa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), sun gudanar da bikin ranar yara ta duniya tare da yin kira ga yaran su guji shaye-shayen miyagun kwayoyi, tashe-tashen hankula, da dabi’un marasa kyau.

Bikin wanda aka gudanar a Birnin Kebbi a ranar Laraba, wani kokari ne na hadin guiwa da AGILE da kungiyar masu yi wa kasa hidima (NYSC) da ke yekuwa kan ilimi.

  • Tsarabar Taron Kolin G20
  • Matatar Dangote Ta Fara Fitar Man Fetur Dinta Zuwa Kasashen Afrika

Bikin ya samu halartar makarantun sakandire guda 10 da suka halarci tarukan kacici-kacici da muhawara a wajen taron bikin.

Babban sakataren ma’aikatar yada labarai da al’adu, Alhaji Buhari Wara, ya nanata kudirin gwamnatin jihar na tallafa wa rayuwar yara ta hanyar ingantaccen ilimi da yanayin Karatu mai kyau.

Ya kuma jaddada cewa jihar na da burin samar wa yara damar samun ilimi mai inganci, kiwon lafiya, tsaftataccen ruwan sha, da muhalli mai kyau.

Labarai Masu Nasaba

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

Hakazalika Alhaji Buhari Wara, ya bukaci yara su mayar da hankali kan karatunsu, su nisanci munanan dabi’u, su tabbatar da tsaron lafiyarsu.

“Yara su ne kashin bayan al’umma,” in ji Wara.

“Yayin da kuka girma, za ku fuskanci kalubale da yawa.

“Ku guje wa shaye-shayen kwayoyi, tashin hankali, da halayen da ba a so, yayin da suke haifar da mummunan sakamako.

“Saboda haka ku mayar da hankali kan karatunku, kuma za ku samu ikon zabar makomarku kuma ku samu hikima.”

Dokta Sahail Sheikh, wakilin UNICEF, ya jaddada sadaukarwar kungiyar wajen yi wa mata da yara hidima, tare da ba su damarmaki a fannoni daban-daban na rayuwa, da suka hada da kiwon lafiya, ilimi, tsaftataccen ruwan sha, hakkin yara, da kariya daga cututtuka masu yaduwa.

Ko’odinetan NYSC reshen Jihar Kebbi, Alhaji Bala Dabo, ya yaba wa Kungiyar UNICEF da Kungiyar CDS ta ilimi bisa shirya gasar kacici-kacici a tsakanin makarantu tare da hadin gwiwar UNICEF.

Kwalejin ‘yan mata da ke Makerar Gwandu ce ta zo na daya a gasar kacici-kacici da maki 60, sai Kwalejin Rayhaan da maki 55, sai makarantar Royal Lead academy da maki 40.

Taken ranar yara ta duniya na bana, “Kyakkyawan Ilimi Yana da Muhimmanci ga Al’umma,” a duk lokacin da aka gudanar da taron, dukkanin makarantun da suka halarci bikin ana ba su takardar shaidar halartar bikin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BikiKebbiUNICEFYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Sakataren FEDECO, Ahmadu Kurfi, Ya Rasu Yana Da Shekaru 93

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa

Related

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

56 minutes ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

15 hours ago
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto
Labarai

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

18 hours ago
Yadda Kwamishinan Kano Ya KarÉ“i Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto
Labarai

Yadda Kwamishinan Kano Ya KarÉ“i Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

18 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 
Da É—umi-É—uminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 

20 hours ago
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50
Labarai

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

21 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa

Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa

LABARAI MASU NASABA

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.