• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bikin Yara Na Duniya Ya Gudana A Kebbi

by Umar Faruk
12 months ago
Yara

Gwamnatin Jihar Kebbi da Asusun Tallafa wa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), sun gudanar da bikin ranar yara ta duniya tare da yin kira ga yaran su guji shaye-shayen miyagun kwayoyi, tashe-tashen hankula, da dabi’un marasa kyau.

Bikin wanda aka gudanar a Birnin Kebbi a ranar Laraba, wani kokari ne na hadin guiwa da AGILE da kungiyar masu yi wa kasa hidima (NYSC) da ke yekuwa kan ilimi.

  • Tsarabar Taron Kolin G20
  • Matatar Dangote Ta Fara Fitar Man Fetur Dinta Zuwa Kasashen Afrika

Bikin ya samu halartar makarantun sakandire guda 10 da suka halarci tarukan kacici-kacici da muhawara a wajen taron bikin.

Babban sakataren ma’aikatar yada labarai da al’adu, Alhaji Buhari Wara, ya nanata kudirin gwamnatin jihar na tallafa wa rayuwar yara ta hanyar ingantaccen ilimi da yanayin Karatu mai kyau.

Ya kuma jaddada cewa jihar na da burin samar wa yara damar samun ilimi mai inganci, kiwon lafiya, tsaftataccen ruwan sha, da muhalli mai kyau.

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

Hakazalika Alhaji Buhari Wara, ya bukaci yara su mayar da hankali kan karatunsu, su nisanci munanan dabi’u, su tabbatar da tsaron lafiyarsu.

“Yara su ne kashin bayan al’umma,” in ji Wara.

“Yayin da kuka girma, za ku fuskanci kalubale da yawa.

“Ku guje wa shaye-shayen kwayoyi, tashin hankali, da halayen da ba a so, yayin da suke haifar da mummunan sakamako.

“Saboda haka ku mayar da hankali kan karatunku, kuma za ku samu ikon zabar makomarku kuma ku samu hikima.”

Dokta Sahail Sheikh, wakilin UNICEF, ya jaddada sadaukarwar kungiyar wajen yi wa mata da yara hidima, tare da ba su damarmaki a fannoni daban-daban na rayuwa, da suka hada da kiwon lafiya, ilimi, tsaftataccen ruwan sha, hakkin yara, da kariya daga cututtuka masu yaduwa.

Ko’odinetan NYSC reshen Jihar Kebbi, Alhaji Bala Dabo, ya yaba wa Kungiyar UNICEF da Kungiyar CDS ta ilimi bisa shirya gasar kacici-kacici a tsakanin makarantu tare da hadin gwiwar UNICEF.

Kwalejin ‘yan mata da ke Makerar Gwandu ce ta zo na daya a gasar kacici-kacici da maki 60, sai Kwalejin Rayhaan da maki 55, sai makarantar Royal Lead academy da maki 40.

Taken ranar yara ta duniya na bana, “Kyakkyawan Ilimi Yana da Muhimmanci ga Al’umma,” a duk lokacin da aka gudanar da taron, dukkanin makarantun da suka halarci bikin ana ba su takardar shaidar halartar bikin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
Manyan Labarai

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
Labarai

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu!
Rahotonni

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

November 7, 2025
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa

Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.