• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Bikin Yara Na Duniya Ya Gudana A Kebbi

by Umar Faruk
7 months ago
in Labarai
0
Yadda Bikin Yara Na Duniya Ya Gudana A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Kebbi da Asusun Tallafa wa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF), sun gudanar da bikin ranar yara ta duniya tare da yin kira ga yaran su guji shaye-shayen miyagun kwayoyi, tashe-tashen hankula, da dabi’un marasa kyau.

Bikin wanda aka gudanar a Birnin Kebbi a ranar Laraba, wani kokari ne na hadin guiwa da AGILE da kungiyar masu yi wa kasa hidima (NYSC) da ke yekuwa kan ilimi.

  • Tsarabar Taron Kolin G20
  • Matatar Dangote Ta Fara Fitar Man Fetur Dinta Zuwa Kasashen Afrika

Bikin ya samu halartar makarantun sakandire guda 10 da suka halarci tarukan kacici-kacici da muhawara a wajen taron bikin.

Babban sakataren ma’aikatar yada labarai da al’adu, Alhaji Buhari Wara, ya nanata kudirin gwamnatin jihar na tallafa wa rayuwar yara ta hanyar ingantaccen ilimi da yanayin Karatu mai kyau.

Ya kuma jaddada cewa jihar na da burin samar wa yara damar samun ilimi mai inganci, kiwon lafiya, tsaftataccen ruwan sha, da muhalli mai kyau.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

Hakazalika Alhaji Buhari Wara, ya bukaci yara su mayar da hankali kan karatunsu, su nisanci munanan dabi’u, su tabbatar da tsaron lafiyarsu.

“Yara su ne kashin bayan al’umma,” in ji Wara.

“Yayin da kuka girma, za ku fuskanci kalubale da yawa.

“Ku guje wa shaye-shayen kwayoyi, tashin hankali, da halayen da ba a so, yayin da suke haifar da mummunan sakamako.

“Saboda haka ku mayar da hankali kan karatunku, kuma za ku samu ikon zabar makomarku kuma ku samu hikima.”

Dokta Sahail Sheikh, wakilin UNICEF, ya jaddada sadaukarwar kungiyar wajen yi wa mata da yara hidima, tare da ba su damarmaki a fannoni daban-daban na rayuwa, da suka hada da kiwon lafiya, ilimi, tsaftataccen ruwan sha, hakkin yara, da kariya daga cututtuka masu yaduwa.

Ko’odinetan NYSC reshen Jihar Kebbi, Alhaji Bala Dabo, ya yaba wa Kungiyar UNICEF da Kungiyar CDS ta ilimi bisa shirya gasar kacici-kacici a tsakanin makarantu tare da hadin gwiwar UNICEF.

Kwalejin ‘yan mata da ke Makerar Gwandu ce ta zo na daya a gasar kacici-kacici da maki 60, sai Kwalejin Rayhaan da maki 55, sai makarantar Royal Lead academy da maki 40.

Taken ranar yara ta duniya na bana, “Kyakkyawan Ilimi Yana da Muhimmanci ga Al’umma,” a duk lokacin da aka gudanar da taron, dukkanin makarantun da suka halarci bikin ana ba su takardar shaidar halartar bikin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BikiKebbiUNICEFYara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsohon Sakataren FEDECO, Ahmadu Kurfi, Ya Rasu Yana Da Shekaru 93

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa

Related

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

7 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

8 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

9 hours ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

11 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

13 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

14 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa

Gwamnatin Kano Ta Miƙa Yara 76 Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Tsadar Rayuwa

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.