ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
1 year ago
Trump

An sake zaben tsohon shugaban Amurka Donald Trump a matsayin shugaban Kasar Amurka a zaben 2024, wanda ya yi nasara a kan mataimakiyar shugaban kasa, Kamala Harris.

 

Wannan nasara ta Trump ta biyo bayan gagarumin zabe wanda ya kawo tsauri sosai tsakanin jam’iyyun siyasa da kuma yankunan Amurka.

ADVERTISEMENT
  • Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
  • Sarkin Musulmi Ya Nemi A Daina Tsine Wa Shugabanni

Sakamakon zaben da aka gudanar ya nuna yadda Trump ya samu kuri’un da suka kai shi hanyar lashe zaben tare da samun rinjayen wakilan zabe na shugaban Kasa (Electoral College).

 

LABARAI MASU NASABA

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Wannan nasara ta kuma fito fili ne daga kuri’un wasu muhimman jihohin da aka sa ido sosai a kansu. Jim kadan bayan ayyana sakamakon, Trump ya gode wa magoya bayansa a wani jawabi da ya gabatar, yana mai cewa “Amurka ta ba mu wata babbar dama da ba a taba ganin irinta ba.”

 

Sakamakon wannan zabe zai ci gaba da jan hankali musamman ganin yadda ya kawo wani sabon shafi a tarihin siyasar Amurka, inda Trump zai zama daya daga cikin tsoffin shugabannin kasa da suka sake komawa kan mulki bayan shekaru hudu.

 

Wannan zabe na shekarar 2024 ya kuma janyo hankalin duniya saboda zai iya kawo sauye-sauye a manufofin Amurka a fannonin tattalin arziki da shige da fice da tsaro da kuma dangantakar Amurka da sauran kasashen waje.

 

Donald Trump ya samu kuri’u 279, yayin da ita kuma Kamala ta samu kuri’u 219.

 

Dama ana bukata ne dantakara ya samu kuri’u 270 na wakilan masu zabe domin lashe zaben na shugaban kasa.

 

Da fari a yammacin ranar Talata ne sakamakon zabe ya fara fitowa fili a zaben shugaban kasa tsakanin mataimakiyar shugaban Amurka Kamala Harris da tsohon shugaban kasar Donald Trump.

 

Dukkan ‘yan takarar biyu sun yi nasarar lashe zaben tun da wuri a wasu jihohi dake zaman tungarsu a zaben mai cike da tarihi da ka iya ganin Amurka ta zabi shugabar kasa mace ta farko.

 

Trump, wanda ke neman komawa fadar White House bayan ya sha kaye a shekarar 2020, ya kwace jiharsa ta Florida, inda ya samu wakilai 30 na jihar. Harris, kamar yadda aka zata, ya samu nasara a kananan jihohi masu yawa a Gabashin Amurka.

 

Dan takarar da zai lashe zaben na bukatar wakilai 270 daga cikin 538 domin ya samu nasara. Wanda ya yi nasara zai fara wa’adin shugaban kasa na shekaru hudu a watan Janairu.

 

Masu sharhi kan harkokin siyasa sun yi hasashen cewa kallo zai koma kan jihohi bakwai ne kacal a fagen siyasa, inda bincike ya nuna ‘yan takarar biyu na tafiya kankankan da juna – wanda hakan ya sa ake ganin mai rabo ne kawai zai samu.

 

A halin yanzu dai ya tabbata Tsohon Shugaban Kasar na Amurka shi ne ya yi nasarar lashe zaben na shekarar 2024, ya yi takwarorinsa na sauran kasashe ke ci gaba da aika masa sakon taya murna.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani
Labarai

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN
Manyan Labarai

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Next Post
Neymar Zai Yi Jinyar Mako Biyu Bayan Ya Sake Samun Rauni

Neymar Zai Yi Jinyar Mako Biyu Bayan Ya Sake Samun Rauni

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

November 14, 2025
Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.