• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An sake zaben tsohon shugaban Amurka Donald Trump a matsayin shugaban Kasar Amurka a zaben 2024, wanda ya yi nasara a kan mataimakiyar shugaban kasa, Kamala Harris.

 

Wannan nasara ta Trump ta biyo bayan gagarumin zabe wanda ya kawo tsauri sosai tsakanin jam’iyyun siyasa da kuma yankunan Amurka.

  • Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
  • Sarkin Musulmi Ya Nemi A Daina Tsine Wa Shugabanni

Sakamakon zaben da aka gudanar ya nuna yadda Trump ya samu kuri’un da suka kai shi hanyar lashe zaben tare da samun rinjayen wakilan zabe na shugaban Kasa (Electoral College).

 

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Wannan nasara ta kuma fito fili ne daga kuri’un wasu muhimman jihohin da aka sa ido sosai a kansu. Jim kadan bayan ayyana sakamakon, Trump ya gode wa magoya bayansa a wani jawabi da ya gabatar, yana mai cewa “Amurka ta ba mu wata babbar dama da ba a taba ganin irinta ba.”

 

Sakamakon wannan zabe zai ci gaba da jan hankali musamman ganin yadda ya kawo wani sabon shafi a tarihin siyasar Amurka, inda Trump zai zama daya daga cikin tsoffin shugabannin kasa da suka sake komawa kan mulki bayan shekaru hudu.

 

Wannan zabe na shekarar 2024 ya kuma janyo hankalin duniya saboda zai iya kawo sauye-sauye a manufofin Amurka a fannonin tattalin arziki da shige da fice da tsaro da kuma dangantakar Amurka da sauran kasashen waje.

 

Donald Trump ya samu kuri’u 279, yayin da ita kuma Kamala ta samu kuri’u 219.

 

Dama ana bukata ne dantakara ya samu kuri’u 270 na wakilan masu zabe domin lashe zaben na shugaban kasa.

 

Da fari a yammacin ranar Talata ne sakamakon zabe ya fara fitowa fili a zaben shugaban kasa tsakanin mataimakiyar shugaban Amurka Kamala Harris da tsohon shugaban kasar Donald Trump.

 

Dukkan ‘yan takarar biyu sun yi nasarar lashe zaben tun da wuri a wasu jihohi dake zaman tungarsu a zaben mai cike da tarihi da ka iya ganin Amurka ta zabi shugabar kasa mace ta farko.

 

Trump, wanda ke neman komawa fadar White House bayan ya sha kaye a shekarar 2020, ya kwace jiharsa ta Florida, inda ya samu wakilai 30 na jihar. Harris, kamar yadda aka zata, ya samu nasara a kananan jihohi masu yawa a Gabashin Amurka.

 

Dan takarar da zai lashe zaben na bukatar wakilai 270 daga cikin 538 domin ya samu nasara. Wanda ya yi nasara zai fara wa’adin shugaban kasa na shekaru hudu a watan Janairu.

 

Masu sharhi kan harkokin siyasa sun yi hasashen cewa kallo zai koma kan jihohi bakwai ne kacal a fagen siyasa, inda bincike ya nuna ‘yan takarar biyu na tafiya kankankan da juna – wanda hakan ya sa ake ganin mai rabo ne kawai zai samu.

 

A halin yanzu dai ya tabbata Tsohon Shugaban Kasar na Amurka shi ne ya yi nasarar lashe zaben na shekarar 2024, ya yi takwarorinsa na sauran kasashe ke ci gaba da aika masa sakon taya murna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana Na Ganin Akwai Kyakkyawar Dama A Dangantakar Sin Da Najeriya

Next Post

Neymar Zai Yi Jinyar Mako Biyu Bayan Ya Sake Samun Rauni

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

2 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

7 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

8 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

9 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

10 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

11 hours ago
Next Post
Neymar Zai Yi Jinyar Mako Biyu Bayan Ya Sake Samun Rauni

Neymar Zai Yi Jinyar Mako Biyu Bayan Ya Sake Samun Rauni

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.