ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 years ago
Trump

An sake zaben tsohon shugaban Amurka Donald Trump a matsayin shugaban Kasar Amurka a zaben 2024, wanda ya yi nasara a kan mataimakiyar shugaban kasa, Kamala Harris.

 

Wannan nasara ta Trump ta biyo bayan gagarumin zabe wanda ya kawo tsauri sosai tsakanin jam’iyyun siyasa da kuma yankunan Amurka.

ADVERTISEMENT
  • Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
  • Sarkin Musulmi Ya Nemi A Daina Tsine Wa Shugabanni

Sakamakon zaben da aka gudanar ya nuna yadda Trump ya samu kuri’un da suka kai shi hanyar lashe zaben tare da samun rinjayen wakilan zabe na shugaban Kasa (Electoral College).

 

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Wannan nasara ta kuma fito fili ne daga kuri’un wasu muhimman jihohin da aka sa ido sosai a kansu. Jim kadan bayan ayyana sakamakon, Trump ya gode wa magoya bayansa a wani jawabi da ya gabatar, yana mai cewa “Amurka ta ba mu wata babbar dama da ba a taba ganin irinta ba.”

 

Sakamakon wannan zabe zai ci gaba da jan hankali musamman ganin yadda ya kawo wani sabon shafi a tarihin siyasar Amurka, inda Trump zai zama daya daga cikin tsoffin shugabannin kasa da suka sake komawa kan mulki bayan shekaru hudu.

 

Wannan zabe na shekarar 2024 ya kuma janyo hankalin duniya saboda zai iya kawo sauye-sauye a manufofin Amurka a fannonin tattalin arziki da shige da fice da tsaro da kuma dangantakar Amurka da sauran kasashen waje.

 

Donald Trump ya samu kuri’u 279, yayin da ita kuma Kamala ta samu kuri’u 219.

 

Dama ana bukata ne dantakara ya samu kuri’u 270 na wakilan masu zabe domin lashe zaben na shugaban kasa.

 

Da fari a yammacin ranar Talata ne sakamakon zabe ya fara fitowa fili a zaben shugaban kasa tsakanin mataimakiyar shugaban Amurka Kamala Harris da tsohon shugaban kasar Donald Trump.

 

Dukkan ‘yan takarar biyu sun yi nasarar lashe zaben tun da wuri a wasu jihohi dake zaman tungarsu a zaben mai cike da tarihi da ka iya ganin Amurka ta zabi shugabar kasa mace ta farko.

 

Trump, wanda ke neman komawa fadar White House bayan ya sha kaye a shekarar 2020, ya kwace jiharsa ta Florida, inda ya samu wakilai 30 na jihar. Harris, kamar yadda aka zata, ya samu nasara a kananan jihohi masu yawa a Gabashin Amurka.

 

Dan takarar da zai lashe zaben na bukatar wakilai 270 daga cikin 538 domin ya samu nasara. Wanda ya yi nasara zai fara wa’adin shugaban kasa na shekaru hudu a watan Janairu.

 

Masu sharhi kan harkokin siyasa sun yi hasashen cewa kallo zai koma kan jihohi bakwai ne kacal a fagen siyasa, inda bincike ya nuna ‘yan takarar biyu na tafiya kankankan da juna – wanda hakan ya sa ake ganin mai rabo ne kawai zai samu.

 

A halin yanzu dai ya tabbata Tsohon Shugaban Kasar na Amurka shi ne ya yi nasarar lashe zaben na shekarar 2024, ya yi takwarorinsa na sauran kasashe ke ci gaba da aika masa sakon taya murna.

Trump
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya
Trump
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Sulaiman
    Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • Sulaiman
    Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

MASU ALAKA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
Ra'ayi Riga

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Next Post
Neymar Zai Yi Jinyar Mako Biyu Bayan Ya Sake Samun Rauni

Neymar Zai Yi Jinyar Mako Biyu Bayan Ya Sake Samun Rauni

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.