ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Musulmi Ya Nemi A Daina Tsine Wa Shugabanni

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmai, Sa’ad Mohammad Abubakar II, ya yi kira ga ‘yan Njeriya da su daina tsine wa shugabanni ko zaginsu, inda ya horesu da su bari Allah ya yi maganinsu a lokacin da ya so.

 

Ya nusar da cewa, babu wani abu mai kyau ko rashinsa da ke dauwama har abada, sai ya karfafi ‘yan Nijeriya da su dukufa wajen ci gaba da yi wa shugabanni da kasar Nijeriya addu’a domin samun zuwa ga tudun mun tsira.

ADVERTISEMENT
  • Sin Ta Samu Fadadar Adadin Sana’o’i Da Ake Yiwa Rajista
  • Li Xi Ya Kai Ziyara Afirka Ta Kudu

Sarkin Musulmi ya kuma yi amfani da wannan damar wajen tunatar da shugabanni da su tuna da ranar tashin alkiyama, inda Allah Madaukakin Sarki zai titse su don su yi bayani filla-filla kan yadda suka gudanar da jagorancin jama’a, kuma, su sani babu wani mahalukin da zai karesu a gaban mahaliccinsu.

Bugu da kari, ya gargadi shugabannin addini da su daina wawantar da hankulan magoya bayansu bisa wata ra’ayi ko muradinsu na kashin kai, inda ya yi bayanin cewa kaso 90 cikin 100 na mutanen da suke sauraron shugabannin addini a masallatai da cocina su na aminta da ababen da suke gaya musu a matsayin hakan ne mafita a garesu.

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

Ya yi bayanin cewa, Allah ne kawai zai ceci kowani mutum. Ya hori jama’a da su ji tsoron Allah su sani akwai ranar sakamako ga komai, sannan, ya ce, komai bai fi karfin Allah ba, don haka a koma gareshi da neman mafita.

Sultan ya yi wannan fadakarwar ne a yayin taron da aka shirya ga malaman da fastoci kan sauyin yanayi da rigingimu a arewacin Nijeriya, wanda reshen kungiyar daidaito da fahimtar juna ta Kaduna ta shirya da hadin gwiwar ‘International Alert’, a ranar Litinin.
“Ku yi imani da bautar da kuke wa Allah ku bar masa komai, ba wai ga waninsa ba. Ka da ku bari wasu su shashantar da ku daga wannan. Abubuwa da dama suna faruwa a kasar nan, mun yi imani kuma dole ne mu koma ga Allah. Mu zurfafa yin addu’o’i ga kasar nan a dukkanin masallatai. Ban ambaci cocina ba ne saboda shugaban CAN yana nan a nan wajen, ina da yakinin zai ce wani abu irin hakan.”

Ya ce, arewacin Nijeriya na fuskantar matsaloli da daman gaske ba kawai ga sauyin yanayi ba, har ma da talauci, matsalar tsaro, dukka a arewaci da aka santa a da baya da zaman lafiya da ci gaba sosai.

Shi ma a nasa jawabin, shugaban kungiyar Kiristoci na kasa (CAN), Dakta D.C. Okoh, ya ce, tabbas akwai sauyin yanayi a arewa, sai ya misalta da rikicin da ke damun jama’a kuma akwai bukatar daukan matakan shawo kan hakan.

Sarkin Musulmi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9
  • Sulaiman
    Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana
  • Sulaiman
    Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil
  • Sulaiman
    Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano
Sarkin Musulmi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Sarkin Musulmi
Manyan Labarai

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Sarkin Musulmi
Labarai

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano
Labarai

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026
Next Post
IFAD

Ofishin Jakadancin Faransa Da Hadin Gwiwar IITA Sun Horar Da Mata 500 Kasuwancin Noma

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Musulmi

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026
Sarkin Musulmi

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

July 27, 2026
Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.