• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Musulmi Ya Nemi A Daina Tsine Wa Shugabanni

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
8 months ago
in Labarai
0
Sarkin Musulmi Ya Nemi A Daina Tsine Wa Shugabanni
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sarkin Musulmai, Sa’ad Mohammad Abubakar II, ya yi kira ga ‘yan Njeriya da su daina tsine wa shugabanni ko zaginsu, inda ya horesu da su bari Allah ya yi maganinsu a lokacin da ya so.

 

Ya nusar da cewa, babu wani abu mai kyau ko rashinsa da ke dauwama har abada, sai ya karfafi ‘yan Nijeriya da su dukufa wajen ci gaba da yi wa shugabanni da kasar Nijeriya addu’a domin samun zuwa ga tudun mun tsira.

  • Sin Ta Samu Fadadar Adadin Sana’o’i Da Ake Yiwa Rajista
  • Li Xi Ya Kai Ziyara Afirka Ta Kudu

Sarkin Musulmi ya kuma yi amfani da wannan damar wajen tunatar da shugabanni da su tuna da ranar tashin alkiyama, inda Allah Madaukakin Sarki zai titse su don su yi bayani filla-filla kan yadda suka gudanar da jagorancin jama’a, kuma, su sani babu wani mahalukin da zai karesu a gaban mahaliccinsu.

Bugu da kari, ya gargadi shugabannin addini da su daina wawantar da hankulan magoya bayansu bisa wata ra’ayi ko muradinsu na kashin kai, inda ya yi bayanin cewa kaso 90 cikin 100 na mutanen da suke sauraron shugabannin addini a masallatai da cocina su na aminta da ababen da suke gaya musu a matsayin hakan ne mafita a garesu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Ya yi bayanin cewa, Allah ne kawai zai ceci kowani mutum. Ya hori jama’a da su ji tsoron Allah su sani akwai ranar sakamako ga komai, sannan, ya ce, komai bai fi karfin Allah ba, don haka a koma gareshi da neman mafita.

Sultan ya yi wannan fadakarwar ne a yayin taron da aka shirya ga malaman da fastoci kan sauyin yanayi da rigingimu a arewacin Nijeriya, wanda reshen kungiyar daidaito da fahimtar juna ta Kaduna ta shirya da hadin gwiwar ‘International Alert’, a ranar Litinin.
“Ku yi imani da bautar da kuke wa Allah ku bar masa komai, ba wai ga waninsa ba. Ka da ku bari wasu su shashantar da ku daga wannan. Abubuwa da dama suna faruwa a kasar nan, mun yi imani kuma dole ne mu koma ga Allah. Mu zurfafa yin addu’o’i ga kasar nan a dukkanin masallatai. Ban ambaci cocina ba ne saboda shugaban CAN yana nan a nan wajen, ina da yakinin zai ce wani abu irin hakan.”

Ya ce, arewacin Nijeriya na fuskantar matsaloli da daman gaske ba kawai ga sauyin yanayi ba, har ma da talauci, matsalar tsaro, dukka a arewaci da aka santa a da baya da zaman lafiya da ci gaba sosai.

Shi ma a nasa jawabin, shugaban kungiyar Kiristoci na kasa (CAN), Dakta D.C. Okoh, ya ce, tabbas akwai sauyin yanayi a arewa, sai ya misalta da rikicin da ke damun jama’a kuma akwai bukatar daukan matakan shawo kan hakan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Samu Fadadar Adadin Sana’o’i Da Ake Yiwa Rajista

Next Post

Ofishin Jakadancin Faransa Da Hadin Gwiwar IITA Sun Horar Da Mata 500 Kasuwancin Noma

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da ɗumi-ɗuminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

5 hours ago
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

7 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

8 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

11 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da Ɗaliban Kaduna Kyauta A Bas

14 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

15 hours ago
Next Post
IFAD

Ofishin Jakadancin Faransa Da Hadin Gwiwar IITA Sun Horar Da Mata 500 Kasuwancin Noma

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.