ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sarkin Musulmi Ya Nemi A Daina Tsine Wa Shugabanni

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmai, Sa’ad Mohammad Abubakar II, ya yi kira ga ‘yan Njeriya da su daina tsine wa shugabanni ko zaginsu, inda ya horesu da su bari Allah ya yi maganinsu a lokacin da ya so.

 

Ya nusar da cewa, babu wani abu mai kyau ko rashinsa da ke dauwama har abada, sai ya karfafi ‘yan Nijeriya da su dukufa wajen ci gaba da yi wa shugabanni da kasar Nijeriya addu’a domin samun zuwa ga tudun mun tsira.

ADVERTISEMENT
  • Sin Ta Samu Fadadar Adadin Sana’o’i Da Ake Yiwa Rajista
  • Li Xi Ya Kai Ziyara Afirka Ta Kudu

Sarkin Musulmi ya kuma yi amfani da wannan damar wajen tunatar da shugabanni da su tuna da ranar tashin alkiyama, inda Allah Madaukakin Sarki zai titse su don su yi bayani filla-filla kan yadda suka gudanar da jagorancin jama’a, kuma, su sani babu wani mahalukin da zai karesu a gaban mahaliccinsu.

Bugu da kari, ya gargadi shugabannin addini da su daina wawantar da hankulan magoya bayansu bisa wata ra’ayi ko muradinsu na kashin kai, inda ya yi bayanin cewa kaso 90 cikin 100 na mutanen da suke sauraron shugabannin addini a masallatai da cocina su na aminta da ababen da suke gaya musu a matsayin hakan ne mafita a garesu.

LABARAI MASU NASABA

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Ya yi bayanin cewa, Allah ne kawai zai ceci kowani mutum. Ya hori jama’a da su ji tsoron Allah su sani akwai ranar sakamako ga komai, sannan, ya ce, komai bai fi karfin Allah ba, don haka a koma gareshi da neman mafita.

Sultan ya yi wannan fadakarwar ne a yayin taron da aka shirya ga malaman da fastoci kan sauyin yanayi da rigingimu a arewacin Nijeriya, wanda reshen kungiyar daidaito da fahimtar juna ta Kaduna ta shirya da hadin gwiwar ‘International Alert’, a ranar Litinin.
“Ku yi imani da bautar da kuke wa Allah ku bar masa komai, ba wai ga waninsa ba. Ka da ku bari wasu su shashantar da ku daga wannan. Abubuwa da dama suna faruwa a kasar nan, mun yi imani kuma dole ne mu koma ga Allah. Mu zurfafa yin addu’o’i ga kasar nan a dukkanin masallatai. Ban ambaci cocina ba ne saboda shugaban CAN yana nan a nan wajen, ina da yakinin zai ce wani abu irin hakan.”

Ya ce, arewacin Nijeriya na fuskantar matsaloli da daman gaske ba kawai ga sauyin yanayi ba, har ma da talauci, matsalar tsaro, dukka a arewaci da aka santa a da baya da zaman lafiya da ci gaba sosai.

Shi ma a nasa jawabin, shugaban kungiyar Kiristoci na kasa (CAN), Dakta D.C. Okoh, ya ce, tabbas akwai sauyin yanayi a arewa, sai ya misalta da rikicin da ke damun jama’a kuma akwai bukatar daukan matakan shawo kan hakan.

Sarkin Musulmi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Sulaiman
    Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya
  • Sulaiman
    Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
  • Sulaiman
    Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela
Sarkin Musulmi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i
Labarai

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Next Post
IFAD

Ofishin Jakadancin Faransa Da Hadin Gwiwar IITA Sun Horar Da Mata 500 Kasuwancin Noma

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.