• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Fasahar Zamani Ke Fadada Ayyukan Dakunan Karatu

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Kimiyya Da Fasahar Sadarwa
0
Yadda Fasahar Zamani Ke Fadada Ayyukan Dakunan Karatu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin yanzu, dakunan karatu (Libraries) ba su zama zallar cibiyar littafan karatu zalla ba; sun kasance masu rungumar fasaha da kuma sabbin hanyoyin da tafiya da zamani daidai da bukatun jama’a.

A zamanin nan na fasaha, dakunan karatu ba su tsaya zallar a zo cikinsu a zauna a dauki littafi a yi karatu kamar yadda aka saba a da can baya ba, yanzu cibiyoyin karatun da dama sun bi ayarin zamani wajen tafiya da zamani da kuma samar da littafai ta yanar gizo, shafukan yanar gizo domin bincike da sauran muhimman hanyoyi da zamani ya zo da su.

  • CBN Ya Bayyana Sunayen Bankuna 41 Da Ya Aminta Da Ingancinsu A Nijeriya 
  • Majalisar Dattawa Za Ta Kafa Dokar Kare Hakkin ‘Yan Aikatau A Nijeriya 

Bugu da kari, dakunan karatun sun kuma kasance cibiyoyin ba da dama ga jama’a domin samun hanyoyin mu’amala da fasahar zamani, tarukan bita, horaswa da kuma ba da dama domin bunkasa hanyoyin hadaka wajen kirkirar sabbin abubuwa ta hanyar zamani.

Ta hanyar runguma da amfani da fasaha, dakunan karatu na iya ci gaba da jan ragamarsu a bangaren ba da dama na yin karatu da taimaka wa jama’a wajen samun bayanai da bunkasa ilimin jama’a.

Wannan canjin ya bai wa dakunan karatu damar ci gaba da kasancewa wurare masu matukar amfani wajen koyon ilimi da fadada ilimi, bincike da saurin samun bayanai a tsakanin jama’a a fadin duniya. Saukin samar wa jama’a da hanyoyin shiga yanar gizo, littafai ta yanar gizo, littafai da ake sauraronsu ta sautin murya, mujallo sun kasance hanyoyin samun ilimi mafi sauki ga masu karatu a kowani lokaci a kuma ko’ina.

Labarai Masu Nasaba

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

Wannan matakin ya kawo wani gagarumin sauyi ta bangaren ‘yancin samun bayanai. Masu amfani da dakunan karatu a yanzu suna da ‘yancin shiga a dama da su wajen koyon karatu da bincike ba tare da wani la’akari da nisan wuri ko kashe kudade ko samun tsangwama wajen neman ilimi ba.

Tafiya da zamani ya kai matakin da dakunan karatu sun iya samar da yanayi mai kyau da sauki da marmari ga masu amfani. A yayin da fasaha ke kara samun gurbin zama, su ma dakunan karatu za su ci gaba da rungumar hanyoyin da fasahan ya zo da su wajen ganin sun tabbatar da ilimi ya samu ga jama’a a zamanin da fasahar zamani ke bunkasa. Bincike ya gano cewa ta hanyar zamanin, dakunan karatu na samun damar saukaka wa jama’a da kuma rage kashe kudade wajen samun ilimi da bincike.

Sai dai kuma duk da wannan gagarumin ci gaba da ake fuskanta, a wasu yankunan ana kallon kamar akwai ‘yan matsalolin da muddin masu ruwa da tsaki ba su dauki matakan shawo kansu ba za a iya samun matsala.

Misali a Nijeriya wasu dakunan karatun na fama da matsalar rashin wadataccen kudin intanet (data) da jama’a za su rika amfani da shi wajen shiga yanar gizo domin bincike da karanta littafai ta yanar gizo. Kazalika, a wasu cibiyoyin akwai karancin na’urori masu kwakwalwa wanda hakan na gurgunta sa’ayin wasu matasa na neman ilimi da bincike.

Duk da yake mafi yawan dakunan karatu sun kasance cibiyoyin koyar da na’ura mai kwakwalwa, amma rashin wadataccen wutar lantarki na zama cikas ga cikan burikan wasu na samun ilimi cikin sauki da hanzari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dakin KaratuFasahar ZamaniKaratu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sarkin Tikau Ya Rasu Yana Da Shekaru 74

Next Post

Nijeriya Na Kara Kaimin Bunkasa Sufurin Jiragen Sama Ta Hanyar Fasahar Tauraron Dan’adam – Keyamo

Related

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

2 months ago
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

4 months ago
Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Hanyoyin Kare Kanka Daga Damfara Ta Intanet

4 months ago
Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet

4 months ago
Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Mantuwa Na Matukar Taimakon Rayuwar Mutane – Masani

9 months ago
Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Yadda Na Kirkiro ‘Brain-chip’ Da Ke Dawo Wa Wadanda Aka Haifa Da Makanta Ganinsu – Elon Musk

9 months ago
Next Post
Yadda Za A Dakile Kitsa Labarun Kanzon Kurege A Nijeriya  -Keyamo

Nijeriya Na Kara Kaimin Bunkasa Sufurin Jiragen Sama Ta Hanyar Fasahar Tauraron Dan’adam – Keyamo

LABARAI MASU NASABA

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

June 27, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

June 27, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

June 27, 2025
Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

Sarkin Yarbawan Funtuwa Ya Nemi A Daƙile Aiyukan Masu Ba ‘Yan Ta’adda Bayanan  Sirri

June 27, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

June 27, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.