• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tinubu Ta Shirya Tsara ‘Yan Nijeriya Da Farfaganda – Atiku

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya, Manyan Labarai
0
Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP kuma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya yi zargin cewa, gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ta shirya tsara ‘yan Nijeriya a wasu kwanaki masu zuwa. 

Ya bayyana cewa Tinubu ya nada masu ba shi sharawa a kan fannin yada labarai sama da 15, saboda su dunga fitar da bayanai marasa inganci kan manufofi gwamnati tare da kawar da hankalin ‘yan Nijeriya kan matsanancin halin da gwamnatinsa ta jefa su a ciki.

  • Bayan Gindaya Wa’adi: Hukumar AGIS Na Tattara Harajin Naira Biliyan Daya A Kullum 

A cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya ce labarin karya ne ake yadawa game da dage haramcin biza da kasar Dubai ta yi wa Nijeriya, amma babu kamshin gaskiya cikin lamarin.

Ya ce wannan shi ne salon gwamnatin Tinubu kuma shugaban jam’iyyarsa.

Atiku ya ce, “Daga bayanan da muka samu, Bola Tinubu na shirin tura farfaganda don wuce gona da iri yayin da yake shirin halartar taron Majalisar Dinkin Duniya. Zai yi ikirarin ya janyo masu zuba jari na kasashen waje da ya kai dala biliyan 100, amma zai kasa bayar da cikakkun bayanai. Wannan duk farfaganda ce. A kasar Indiya, ya yi ikirarin cewa sun karbi hannun jari sama da dala biliyan 14 kamar yadda magabacinsa, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi a shekarar 2018 cewa ya karbi na dala biliyan 6. Wannan ba komai ba ne illa saka hannun jari na fatar baki.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

“A watan da ya gabata, kamfanin NNPC ya yi ikirarin cewa ya samu rancen dala biliyan 3 da zai taimaka wajen daidaita darajar naira. Mun bayyana cewa duk wannan wata dabara ce ta yaudarar ‘yan Nijeriya. Yanzu dai mun tabbatar da cewa naira na kara durkushewa, wanda a yanzu haka dala ta kusan naira1,000 a kasuwar bayan fage.

“Bayan tafiyarsa zuwa Dubai, Tinubu ya yi ikirarin cewa an dage takunkumin haramcin biza nan take. Yanzu haka sun sauya sheka bayan da hukumomin kasar Dubai suka bayyana cewa labarin karya ne. Irin wannan abin kunya ne ga Nijeriya wanda gwamnati ke ci gaba da jawowa a wannan mulki.

“Duk da ya kasa inganta harkokin tattalin arzikin kasa, amma ya nada masu ba shi shawara kan harkokin yada labarai har guda 15, maimakon ya nada masana tattalin arziki.

“Daga cikin jerin masu ba shi shawara kan harkokin yada labarai akwai da sadarwa akwai: Tunde Rahman,Tope Ajayi, Abdulaziz Abdulaziz, Otega Ogara, Segun Dada da Nosa Asemota .

Sauran su ne: Sunday Moses, Taiwo Okonlawon, Moremi Ojudu, Tanko Yakasai, Chioma Nweze, Abiodun Essiet, Abdulhamid Yahaya Abba da kuma Emmanuella Eduozor. Baya ga wadannan akwai kuma ministan yada labarai da suran wasu nade-nade a ma’aikatan domin yada farfaganda.”

Ya bukaci ‘yan Nijeriya su ci gaba da hakuri a daidai lokacin da kotun koli ke shirin zantar da hukunci kan zaben shugaban kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtikuPDPSiyasaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bunkasa Kimiyya Da Fasaha: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasar Cuba

Next Post

Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

8 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

14 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

19 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

23 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

24 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

2 days ago
Next Post
Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.