• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tinubu Ta Shirya Tsara ‘Yan Nijeriya Da Farfaganda – Atiku

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya, Manyan Labarai
0
Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP kuma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya yi zargin cewa, gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu ta shirya tsara ‘yan Nijeriya a wasu kwanaki masu zuwa. 

Ya bayyana cewa Tinubu ya nada masu ba shi sharawa a kan fannin yada labarai sama da 15, saboda su dunga fitar da bayanai marasa inganci kan manufofi gwamnati tare da kawar da hankalin ‘yan Nijeriya kan matsanancin halin da gwamnatinsa ta jefa su a ciki.

  • Bayan Gindaya Wa’adi: Hukumar AGIS Na Tattara Harajin Naira Biliyan Daya A Kullum 

A cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman kan harkokin sadarwa, Phrank Shaibu, ya ce labarin karya ne ake yadawa game da dage haramcin biza da kasar Dubai ta yi wa Nijeriya, amma babu kamshin gaskiya cikin lamarin.

Ya ce wannan shi ne salon gwamnatin Tinubu kuma shugaban jam’iyyarsa.

Atiku ya ce, “Daga bayanan da muka samu, Bola Tinubu na shirin tura farfaganda don wuce gona da iri yayin da yake shirin halartar taron Majalisar Dinkin Duniya. Zai yi ikirarin ya janyo masu zuba jari na kasashen waje da ya kai dala biliyan 100, amma zai kasa bayar da cikakkun bayanai. Wannan duk farfaganda ce. A kasar Indiya, ya yi ikirarin cewa sun karbi hannun jari sama da dala biliyan 14 kamar yadda magabacinsa, tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi a shekarar 2018 cewa ya karbi na dala biliyan 6. Wannan ba komai ba ne illa saka hannun jari na fatar baki.

Labarai Masu Nasaba

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

“A watan da ya gabata, kamfanin NNPC ya yi ikirarin cewa ya samu rancen dala biliyan 3 da zai taimaka wajen daidaita darajar naira. Mun bayyana cewa duk wannan wata dabara ce ta yaudarar ‘yan Nijeriya. Yanzu dai mun tabbatar da cewa naira na kara durkushewa, wanda a yanzu haka dala ta kusan naira1,000 a kasuwar bayan fage.

“Bayan tafiyarsa zuwa Dubai, Tinubu ya yi ikirarin cewa an dage takunkumin haramcin biza nan take. Yanzu haka sun sauya sheka bayan da hukumomin kasar Dubai suka bayyana cewa labarin karya ne. Irin wannan abin kunya ne ga Nijeriya wanda gwamnati ke ci gaba da jawowa a wannan mulki.

“Duk da ya kasa inganta harkokin tattalin arzikin kasa, amma ya nada masu ba shi shawara kan harkokin yada labarai har guda 15, maimakon ya nada masana tattalin arziki.

“Daga cikin jerin masu ba shi shawara kan harkokin yada labarai akwai da sadarwa akwai: Tunde Rahman,Tope Ajayi, Abdulaziz Abdulaziz, Otega Ogara, Segun Dada da Nosa Asemota .

Sauran su ne: Sunday Moses, Taiwo Okonlawon, Moremi Ojudu, Tanko Yakasai, Chioma Nweze, Abiodun Essiet, Abdulhamid Yahaya Abba da kuma Emmanuella Eduozor. Baya ga wadannan akwai kuma ministan yada labarai da suran wasu nade-nade a ma’aikatan domin yada farfaganda.”

Ya bukaci ‘yan Nijeriya su ci gaba da hakuri a daidai lokacin da kotun koli ke shirin zantar da hukunci kan zaben shugaban kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCAtikuPDPSiyasaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bunkasa Kimiyya Da Fasaha: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasar Cuba

Next Post

Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

Related

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

6 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

7 hours ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

8 hours ago
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa
Manyan Labarai

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

9 hours ago
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

19 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

21 hours ago
Next Post
Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

Cristiano Ronaldo Ya Zura Kwallaye Uku Rigis A Wasansu Da Al Ahl

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

June 5, 2025
Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.