• English
  • Business News
Wednesday, May 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba Ke Ruruta Ayyukan Ta’addanci

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Hakar Ma’adanai Ba Bisa Ka’ida Ba Ke Ruruta Ayyukan Ta’addanci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanan nan Ministan Ma’adanai, Mista Dele Alake, ya bayyana alakar hakar ma’adanai da bisa ka’ida ba da ayyukan ta’addanci a kasar nan. A ta bakinsa, “Yawancin ayyukan ta’addanci da na ‘yan bindiga masu harkokin hakar ma’adanai ba bisa ka’idaba suke daukar nauyinsu a Nijeriya. Ba wai wadanda suke aikin hakar ainihin ma’adanan ba ne amma manyan masu kudi ne a sassan Nijeriya suke daukar nauyin ta’addancin”. A ra’ayinmu da muka wallafa a wani lokaci a baya mun yi irin wannan bayanin.

Mun sake dawo da sharhin ne don ya zama kalubale ga gwamnati domin ta samo hanyar warware matsalar. Dole ne a fallasa tare da kunyata wadannan mutanen. Minista Alake zai iya jagorantar wannan fafatawar.

  • Jarin Waje Na Kai Tsaye Dake Shigowa Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 1.04 Cikin Watanni 11 Na Farkon Bana
  • Gwamnan Zamfara Ya Gabatar Da Kasafin N432.5b Shekarar 2024

Al’amarin da ya shafi dangantakar ayyukan ta’addanci da hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a Nijeriya ya kara fitowa fili ne a wani rahoto da wata jaridar kasar Birtaniya ta ruwaito kan yadda ‘yan kasuwar kasar Sin suka mamaye harkar hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba kuma suke tallafa wa masu ayyukan ta’addanci a sassan Nijeriya. Jaridar ta kuma kara da cewa, ‘yan kasar Chanan suna cimma wannan buri nasu ne ta hanyar bayar da cin hanci ga wasu bangarori da al’ummar Nijeriya.

Amma kuma nan take ofishin jakadancin kasar Chana a Nijeriya ya karyata wannan zargin, tare da bayyana cewa babu cikakkun hujjoji na danganta kasar Chana da ayyukan masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

Yana da matukar muhimmaci a fahimci cewa, ba wannan ne karo na farko ba da ‘yan Nijeriya ke lura da cewa, ayyukan masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba yana taimaka wa ayyukan ‘yan ta’adda a sassan Nijeriya. Wannan yana kara fitowa fili ne in aka lura da yadda ‘yan bindigar ke fuskantar jami’an tsaronmu da makamai na zamani masu karfi da kuma yadda suke yada farfaganda don dakile gaskiyar halin da ake ciki. A lokuta da dama wadannan ‘yan ta’addar suna tafka ayyukan ta’addanci ba tare da an hukunta su ba.

Labarai Masu Nasaba

Hajji: NAHCON Ta Kammala Jigilar Kashi 77 Na Mahajjatan Nijeriya Zuwa Saudiyya 

Tattalin Arziƙin Nijeriya Na Ƙara Farfaɗowa – Gwamnan CBN

A matsayinmu na gidan jarida, mun yi imanin cewa, ba zai yiwu a ce, wadannan masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba suna aikata ayyukan ta’addanci ba tare da an hukunta su ba, ya kamata hukumar da ke bayar da izinin hakar ma’adanai ta soke lasisin wadannan kamfanonin da ake zargi in ba haka ba to lallai dole ministan ma’adanai ya fito fili ya yi bayani mai gamsarwa a kan lamarin.

Tun da farko mun kafa ayar tambaya a kan yadda hamshakan masu kudi ke tafiyar da harkar hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, amma kuma idan har akwai hannun wasu kasashen waje a ayuyykan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba to mun san hakan ba zai taba yiwuwa ba sai an samu hadin kan ‘yan Nijeriya.

Yana da matukar muhimmnanci a fahimmci cewa, Nijeriya na da mutane da kowacce al’umma ke mutuntawa suna kuma daukar su da matukar muhimmanci, irin wadannan mutane ne suke daukar nauyin shigowar ‘yan kasashen waje ta hanyar samar musu da Biza da sauran ka’idojin da suke bukatar cikawa, in ma sun samu matsala su ne dai ke tabbatar da ba a hukunta su ba a lokuta da dama. Wannan ne yake kara bayyana mana ainihin dalilin da ya sa suka samu hanyar shigowa cikin kasa tun da farko.

Harkar hakar ma’adanai ba wata abu ba ne da za a iya yi a boye, abu ce da ke bukatar manyan kayan aiki da ma’aikata na cikin gida da kasashen waje yana kuma bukatar zuba jari mai yawan gaske. Ana kuma fitar da abin da aka samu ta hanyoyin shiga da fita kasar nan (ta kasa, ruwa da ta sama). Akwai kuma jami’ai da hukumomin da aka dora wa alhakin kula da wadanna kafofi, shin suna sane da ayyuykan masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba ko kuma suna yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ne?

In har ta hanyar ayyukan hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba Nijeriya na asarar kudaden shiga to mene ne jami’an tsaronmu da sauran hukumomin gwamnati ke yi don dakile ayyukan masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa?

A ra’ayinmmu, babu wani aiki na masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba a halin yanzu sai da kawai tare da ayyukan wasu tsageru da suke amfani da tabarbarewar harkoki a kasa na abin da ya shafi cin hanci da rashin iya gudanar da aiki a ma’aikatun gwamnnati don cutar da tattalin arzikin kasa, suna daukar nauyin ‘yan ta’adda don su dauke hankali daga ainihin abin da ke faruwa a yankunan kasar nan inda wasu ‘yan kalilan ke tatsar dukiyoyin kasa.

A duk lokacin da aka samu hannun kasashen waje a harkokin hakar ma’adanai dole a fuskanci matsalolin tsaro, muna da darussa daga abin da ya faru a kasashe irin su Saliyo da Kongo. Duk da cewa, majalisar dinkin duniya na da hanyoyin da take fuskantar irin wadannan matsalolin. Ya kamata kafin tarayyar kasashen duniya su kawo mana dauki dole gwamnatin Nijeriya ta amince da cewa, lallai akwai matsala a bangaren hakar ma’adanai a kasar nan, ta kuma dauki matakin da suka dace don magance yadda masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ke cin karensu babu babbaka, dole gwamnati ta toshe duk wata kafa kafin a kai ga dora wani laifi a kan wani. Ya kamata gwamnati ta dauki kudurin fuskantar lamarin kai tsaye ba tare da nuna tsoro ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Zantawa Da Sin Lokaci Ya Yi Da Philippines Ta Gane Kuskurenta

Next Post

Rayuwar ‘Yan Jari-bola Bayan Fatattakar Su A Abuja

Related

Hajjin Bana: Jihar Filato Ta Ba Da Kyautar Kujera 500 Da Tallafin Miliyan 2 Ga Duk Maniyyaci
Manyan Labarai

Hajji: NAHCON Ta Kammala Jigilar Kashi 77 Na Mahajjatan Nijeriya Zuwa Saudiyya 

8 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Na Ƙara Farfaɗowa – Gwamnan CBN
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Na Ƙara Farfaɗowa – Gwamnan CBN

12 hours ago
Na Kwana A Marte Ne Don Ƙarfafa Gwiwar Jama’a Bayan Harin Boko Haram – Zulum
Manyan Labarai

Na Kwana A Marte Ne Don Ƙarfafa Gwiwar Jama’a Bayan Harin Boko Haram – Zulum

16 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna

1 day ago
Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun

1 day ago
Ana Zargin ‘Yansanda Da Keta Haddin Dan Jarida A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja

1 day ago
Next Post
Rayuwar ‘Yan Jari-bola Bayan Fatattakar Su A Abuja

Rayuwar 'Yan Jari-bola Bayan Fatattakar Su A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

Farar Dabarar Da Tsoffin Masana’antu Ke Yi A Kasar Sin Don Tafiya Da Zamani

May 21, 2025
Bayan Shekaru 42 Babu Kofi, Tottenham Ta Lashe Gasar Europa League Akan Manchester United 

Bayan Shekaru 42 Babu Kofi, Tottenham Ta Lashe Gasar Europa League Akan Manchester United 

May 21, 2025
Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar Biliyan ₦2.6bn

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar Biliyan ₦2.6bn

May 21, 2025
Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

Shirye-shiryen Shugaba Tinubu Suna Buɗe Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

May 21, 2025
Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka

May 21, 2025
Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

Sin Tana Da Karfi Wajen Tinkarar Hadari Da Kalubale A Fannoni Daban Daban

May 21, 2025
Sabbin Ministoci

Boko Haram: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kafa Sansanin Sojoji A Hong Ta Jihar Adamawa

May 21, 2025
Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

Sin Ta Soki Yunkurin Amurka Na Hana Amfani Da Chips Kirar Kasar Sin

May 21, 2025
Sin Ta Fitar Da Fim Dake Bayyana Al’amaru Na Gaske Bisa Taken “Gajimare A Doron Kasa” 

Sin Ta Fitar Da Fim Dake Bayyana Al’amaru Na Gaske Bisa Taken “Gajimare A Doron Kasa” 

May 21, 2025
Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo

Rashin Tsaro: Matasa Sun Yi Zanga-zangar Toshe Babbar Hanya Saboda Satar Mutane A Edo

May 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.