• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jaridar Daily Champion Ta Karrama Shugaban NPA, Mohammed Bello-Koko

by Bello Hamza
2 years ago
in Rahotonni
0
Yadda Jaridar Daily Champion Ta Karrama Shugaban NPA, Mohammed Bello-Koko
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanakin baya ne kamfanin jaridar ‘Daily Champion’ ya karrama shugaban Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa Nijeriya (NPA), Mohammed Bello-Koko, da kambun jagora kuma shugaba a bangaren harkar safara da mu’amala da tashohin jiragen ruwan Nijeriya na shekarar 2022.

Wannan karramawar na zuwa ne saboda jajircewarsa a wajen bunkasa harkokin gudanarwa na tashoshin jiragen Ruwan Nijeriya (NPA) musamman tashoshin da ke can cikin teku, da kuma yadda aka samu karin kudaden shiga da hukumar ke zubawa a asusun gwamnatin tarayya, wani abin da aka dade ba a samu irinsa ba, haka kuma ya yi kokari a wajen samar da sabbin kayan aiki a tashoshin ruwan Nijeriya wadanda suka yi daidai da yadda ake samu a kasashen duniya, wanda hakan ya taimaka wajen daga darajar Nijeriya a kasashen duniya.

  • Da Ikon Allah Babu Bacci Ko Daga Kafa Sai Na Shawo Kan Matsalar Tsaro – Gwamnan Zamfara

Wasu dalilai da jaridar ta ‘Daily Champion’ ta bayyan a matsayin abin da suka sa hukumar gudanarwar jaridar ta karrama Mohammed Bello Koko sun hada da yadda ya samar da wani tsari ha musanmman da ake kira da ‘Port Community System (PCS)’ wanda haka ya taimaka wajen samar da tsari guda daya na gudanar da harkokin tashoshin ruwa ta yadda aka yi maganin maimaita aiki wanda a baya sune ke haifar da bata lokaci da jinkiri wajen sallamar abokan huldar, masana sun kuma yaba da wannan kokarin don ya taimaka wajen mayar hankali ga tashoshin jiragen ruwa dake a yankunan kudancin kasar nan.

Hukumar gudanarwar kamfanin jaridar ‘Daily Champion’ ta bayyana cewa, ta karramar Bello-Koko ne saboda yadda ya samar da sabbin tsare-tsare a harkokin gudanarwar hkumar NPA wanda hakan ya matukar taimakwa wajen bunkasa hulumar a bangarori da dama da suka hada da tattalin arziki, zamantaewwa da jindadin ma’aikata, musamman kuma yadda aka samu karin kudaden shiga ga kasar mu Nijeriya.

Hukumar gudanarwar jaridar Daily Champion sun kwatanta Mohammed Bello Koko da wani gogagge da ya yi fice a wajen gudanar da hukumar NPA ya kuma yi fintinkau a wajen tsimin kudaden hukumar, an kuma kwatantan shi da mutum wanda ya kama kansa ya rike mutuncinsa a rayuwarsa na yau da kulum da kuma yanayin aikinsa na gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Shugaban kamfanin na jaridar Daily Champion, Dakta Nwadiuto Iheakanwa, ya bayyana cewa, irin jajircewar shugaban NPA Bello Koko da yadda yake gudanar da shugabancin hukumar ya taimaka wajen bunkasa harkokin tashoshin ruwan Nijeriya ya kuma daga darajar NPA a idon duniya fiye da yadda ake tunani, musamman abin da ba a taba gani ba a ‘yan shekarun nan.

Ya kuma kara da cewa, ayyukan alhairin da Mohammed Bello Koko ya yi sun hada da samar da sabbin gine-ginen ofishoshin ma’aikata da tabbatar da biyan hakokin ma’aikata wanda da wahala a samu wata hukumar gwamnati da take da matsayi irin wannan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Dangantakar Sin Da Amurka Za Ta Sauya Bayan Ziyarar Antony Blinken A Sin?

Next Post

Hadiza Bala Usman Ta Gargadi Masu Gangamin Bata Mata Suna

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Hadiza Bala Usman Ta Gargadi Masu Gangamin Bata Mata Suna

Hadiza Bala Usman Ta Gargadi Masu Gangamin Bata Mata Suna

LABARAI MASU NASABA

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.