• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jaridar Daily Champion Ta Karrama Shugaban NPA, Mohammed Bello-Koko

by Bello Hamza
2 years ago
in Rahotonni
0
Yadda Jaridar Daily Champion Ta Karrama Shugaban NPA, Mohammed Bello-Koko
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanakin baya ne kamfanin jaridar ‘Daily Champion’ ya karrama shugaban Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa Nijeriya (NPA), Mohammed Bello-Koko, da kambun jagora kuma shugaba a bangaren harkar safara da mu’amala da tashohin jiragen ruwan Nijeriya na shekarar 2022.

Wannan karramawar na zuwa ne saboda jajircewarsa a wajen bunkasa harkokin gudanarwa na tashoshin jiragen Ruwan Nijeriya (NPA) musamman tashoshin da ke can cikin teku, da kuma yadda aka samu karin kudaden shiga da hukumar ke zubawa a asusun gwamnatin tarayya, wani abin da aka dade ba a samu irinsa ba, haka kuma ya yi kokari a wajen samar da sabbin kayan aiki a tashoshin ruwan Nijeriya wadanda suka yi daidai da yadda ake samu a kasashen duniya, wanda hakan ya taimaka wajen daga darajar Nijeriya a kasashen duniya.

  • Da Ikon Allah Babu Bacci Ko Daga Kafa Sai Na Shawo Kan Matsalar Tsaro – Gwamnan Zamfara

Wasu dalilai da jaridar ta ‘Daily Champion’ ta bayyan a matsayin abin da suka sa hukumar gudanarwar jaridar ta karrama Mohammed Bello Koko sun hada da yadda ya samar da wani tsari ha musanmman da ake kira da ‘Port Community System (PCS)’ wanda haka ya taimaka wajen samar da tsari guda daya na gudanar da harkokin tashoshin ruwa ta yadda aka yi maganin maimaita aiki wanda a baya sune ke haifar da bata lokaci da jinkiri wajen sallamar abokan huldar, masana sun kuma yaba da wannan kokarin don ya taimaka wajen mayar hankali ga tashoshin jiragen ruwa dake a yankunan kudancin kasar nan.

Hukumar gudanarwar kamfanin jaridar ‘Daily Champion’ ta bayyana cewa, ta karramar Bello-Koko ne saboda yadda ya samar da sabbin tsare-tsare a harkokin gudanarwar hkumar NPA wanda hakan ya matukar taimakwa wajen bunkasa hulumar a bangarori da dama da suka hada da tattalin arziki, zamantaewwa da jindadin ma’aikata, musamman kuma yadda aka samu karin kudaden shiga ga kasar mu Nijeriya.

Hukumar gudanarwar jaridar Daily Champion sun kwatanta Mohammed Bello Koko da wani gogagge da ya yi fice a wajen gudanar da hukumar NPA ya kuma yi fintinkau a wajen tsimin kudaden hukumar, an kuma kwatantan shi da mutum wanda ya kama kansa ya rike mutuncinsa a rayuwarsa na yau da kulum da kuma yanayin aikinsa na gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Shugaban kamfanin na jaridar Daily Champion, Dakta Nwadiuto Iheakanwa, ya bayyana cewa, irin jajircewar shugaban NPA Bello Koko da yadda yake gudanar da shugabancin hukumar ya taimaka wajen bunkasa harkokin tashoshin ruwan Nijeriya ya kuma daga darajar NPA a idon duniya fiye da yadda ake tunani, musamman abin da ba a taba gani ba a ‘yan shekarun nan.

Ya kuma kara da cewa, ayyukan alhairin da Mohammed Bello Koko ya yi sun hada da samar da sabbin gine-ginen ofishoshin ma’aikata da tabbatar da biyan hakokin ma’aikata wanda da wahala a samu wata hukumar gwamnati da take da matsayi irin wannan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Dangantakar Sin Da Amurka Za Ta Sauya Bayan Ziyarar Antony Blinken A Sin?

Next Post

Hadiza Bala Usman Ta Gargadi Masu Gangamin Bata Mata Suna

Related

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

13 hours ago
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

23 hours ago
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

2 days ago
Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano
Rahotonni

Yadda Sanata Barau Ke Samar da Masana Don Ci Gaban Kano

2 days ago
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu
Rahotonni

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

1 week ago
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba
Rahotonni

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

1 week ago
Next Post
Hadiza Bala Usman Ta Gargadi Masu Gangamin Bata Mata Suna

Hadiza Bala Usman Ta Gargadi Masu Gangamin Bata Mata Suna

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.