• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jaridar Daily Champion Ta Karrama Shugaban NPA, Mohammed Bello-Koko

by Bello Hamza
2 years ago
NPA

Kwanakin baya ne kamfanin jaridar ‘Daily Champion’ ya karrama shugaban Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa Nijeriya (NPA), Mohammed Bello-Koko, da kambun jagora kuma shugaba a bangaren harkar safara da mu’amala da tashohin jiragen ruwan Nijeriya na shekarar 2022.

Wannan karramawar na zuwa ne saboda jajircewarsa a wajen bunkasa harkokin gudanarwa na tashoshin jiragen Ruwan Nijeriya (NPA) musamman tashoshin da ke can cikin teku, da kuma yadda aka samu karin kudaden shiga da hukumar ke zubawa a asusun gwamnatin tarayya, wani abin da aka dade ba a samu irinsa ba, haka kuma ya yi kokari a wajen samar da sabbin kayan aiki a tashoshin ruwan Nijeriya wadanda suka yi daidai da yadda ake samu a kasashen duniya, wanda hakan ya taimaka wajen daga darajar Nijeriya a kasashen duniya.

  • Da Ikon Allah Babu Bacci Ko Daga Kafa Sai Na Shawo Kan Matsalar Tsaro – Gwamnan Zamfara

Wasu dalilai da jaridar ta ‘Daily Champion’ ta bayyan a matsayin abin da suka sa hukumar gudanarwar jaridar ta karrama Mohammed Bello Koko sun hada da yadda ya samar da wani tsari ha musanmman da ake kira da ‘Port Community System (PCS)’ wanda haka ya taimaka wajen samar da tsari guda daya na gudanar da harkokin tashoshin ruwa ta yadda aka yi maganin maimaita aiki wanda a baya sune ke haifar da bata lokaci da jinkiri wajen sallamar abokan huldar, masana sun kuma yaba da wannan kokarin don ya taimaka wajen mayar hankali ga tashoshin jiragen ruwa dake a yankunan kudancin kasar nan.

Hukumar gudanarwar kamfanin jaridar ‘Daily Champion’ ta bayyana cewa, ta karramar Bello-Koko ne saboda yadda ya samar da sabbin tsare-tsare a harkokin gudanarwar hkumar NPA wanda hakan ya matukar taimakwa wajen bunkasa hulumar a bangarori da dama da suka hada da tattalin arziki, zamantaewwa da jindadin ma’aikata, musamman kuma yadda aka samu karin kudaden shiga ga kasar mu Nijeriya.

Hukumar gudanarwar jaridar Daily Champion sun kwatanta Mohammed Bello Koko da wani gogagge da ya yi fice a wajen gudanar da hukumar NPA ya kuma yi fintinkau a wajen tsimin kudaden hukumar, an kuma kwatantan shi da mutum wanda ya kama kansa ya rike mutuncinsa a rayuwarsa na yau da kulum da kuma yanayin aikinsa na gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Shugaban kamfanin na jaridar Daily Champion, Dakta Nwadiuto Iheakanwa, ya bayyana cewa, irin jajircewar shugaban NPA Bello Koko da yadda yake gudanar da shugabancin hukumar ya taimaka wajen bunkasa harkokin tashoshin ruwan Nijeriya ya kuma daga darajar NPA a idon duniya fiye da yadda ake tunani, musamman abin da ba a taba gani ba a ‘yan shekarun nan.

Ya kuma kara da cewa, ayyukan alhairin da Mohammed Bello Koko ya yi sun hada da samar da sabbin gine-ginen ofishoshin ma’aikata da tabbatar da biyan hakokin ma’aikata wanda da wahala a samu wata hukumar gwamnati da take da matsayi irin wannan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Hadiza Bala Usman Ta Gargadi Masu Gangamin Bata Mata Suna

Hadiza Bala Usman Ta Gargadi Masu Gangamin Bata Mata Suna

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
NPA

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.