ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jaridar Daily Champion Ta Karrama Shugaban NPA, Mohammed Bello-Koko

by Bello Hamza
3 years ago
NPA

Kwanakin baya ne kamfanin jaridar ‘Daily Champion’ ya karrama shugaban Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa Nijeriya (NPA), Mohammed Bello-Koko, da kambun jagora kuma shugaba a bangaren harkar safara da mu’amala da tashohin jiragen ruwan Nijeriya na shekarar 2022.

Wannan karramawar na zuwa ne saboda jajircewarsa a wajen bunkasa harkokin gudanarwa na tashoshin jiragen Ruwan Nijeriya (NPA) musamman tashoshin da ke can cikin teku, da kuma yadda aka samu karin kudaden shiga da hukumar ke zubawa a asusun gwamnatin tarayya, wani abin da aka dade ba a samu irinsa ba, haka kuma ya yi kokari a wajen samar da sabbin kayan aiki a tashoshin ruwan Nijeriya wadanda suka yi daidai da yadda ake samu a kasashen duniya, wanda hakan ya taimaka wajen daga darajar Nijeriya a kasashen duniya.

  • Da Ikon Allah Babu Bacci Ko Daga Kafa Sai Na Shawo Kan Matsalar Tsaro – Gwamnan Zamfara

Wasu dalilai da jaridar ta ‘Daily Champion’ ta bayyan a matsayin abin da suka sa hukumar gudanarwar jaridar ta karrama Mohammed Bello Koko sun hada da yadda ya samar da wani tsari ha musanmman da ake kira da ‘Port Community System (PCS)’ wanda haka ya taimaka wajen samar da tsari guda daya na gudanar da harkokin tashoshin ruwa ta yadda aka yi maganin maimaita aiki wanda a baya sune ke haifar da bata lokaci da jinkiri wajen sallamar abokan huldar, masana sun kuma yaba da wannan kokarin don ya taimaka wajen mayar hankali ga tashoshin jiragen ruwa dake a yankunan kudancin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Hukumar gudanarwar kamfanin jaridar ‘Daily Champion’ ta bayyana cewa, ta karramar Bello-Koko ne saboda yadda ya samar da sabbin tsare-tsare a harkokin gudanarwar hkumar NPA wanda hakan ya matukar taimakwa wajen bunkasa hulumar a bangarori da dama da suka hada da tattalin arziki, zamantaewwa da jindadin ma’aikata, musamman kuma yadda aka samu karin kudaden shiga ga kasar mu Nijeriya.

Hukumar gudanarwar jaridar Daily Champion sun kwatanta Mohammed Bello Koko da wani gogagge da ya yi fice a wajen gudanar da hukumar NPA ya kuma yi fintinkau a wajen tsimin kudaden hukumar, an kuma kwatantan shi da mutum wanda ya kama kansa ya rike mutuncinsa a rayuwarsa na yau da kulum da kuma yanayin aikinsa na gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Shugaban kamfanin na jaridar Daily Champion, Dakta Nwadiuto Iheakanwa, ya bayyana cewa, irin jajircewar shugaban NPA Bello Koko da yadda yake gudanar da shugabancin hukumar ya taimaka wajen bunkasa harkokin tashoshin ruwan Nijeriya ya kuma daga darajar NPA a idon duniya fiye da yadda ake tunani, musamman abin da ba a taba gani ba a ‘yan shekarun nan.

Ya kuma kara da cewa, ayyukan alhairin da Mohammed Bello Koko ya yi sun hada da samar da sabbin gine-ginen ofishoshin ma’aikata da tabbatar da biyan hakokin ma’aikata wanda da wahala a samu wata hukumar gwamnati da take da matsayi irin wannan.

NPA
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Hadiza Bala Usman Ta Gargadi Masu Gangamin Bata Mata Suna

Hadiza Bala Usman Ta Gargadi Masu Gangamin Bata Mata Suna

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.