ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Karancin Taki Da Tsadarsa Suka Kawo Cikas Ga Noman Daminar Bana

by Abubakar Abba
4 years ago
Cikas

Masana fannin noma a Nijeriya na ci gaba da tofa albarkacin bakin su kan yadda, fannin ya samu koma-baya saboda karancin takin zamani da tsadarsa a daminar bana.

Har ila yau, sun yi nuni da cewa, karancin da kuma tsadar ta takin, zai haifar gibi a fannin da kuma shafar tattalin arzikin Nijeriya.

  • Kudin Da NNPC Ke Kashewa A Tallafin Mai Ya Wuce Kima – Hamid Ali
  • Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wani Masallaci Ya Kashe Akalla Mutane 18 A Afganistan

Kuma wadannan matsalolin, a cewar kwararru na janyo gibi ga irin amfanin gonar da manoman ke samarwa.

ADVERTISEMENT

A cewarsu, a wasu shekarun baya, mahukunta a kasar sun samar da takin wadatacece kuma a cikin rahusa, amma a yanzu takin ya zama Gwal.

Sun kara da cewa, matsalar ta fi shafar manoman da ke yin noma a karkara, inda samun takin ke ci gaba da kara zamar masu babbar matsala.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

“A wasu shekarun baya, mahukunta a kasar sun samar da takin wadatacece kuma a cikin sauki, amma a yanzu takin ya zama Gwal”.

Sun bayyan cewa, cin hanci da rashawa a tsarin na samar da takin, na daya daga cikin kalubalen da ake fuskanta na samar da wadataccen sa a kasar.

Duk da cewa, mahukunta a matakan gwamantin uku na kasar sun shelanta cewa, sun samar da takin a cin farashi mai sauki, amma manoman ba su gani a kasa ba, musaman ganin yadda tsadar ta sa musamman ta hana manoman kasar musamman kanana iya sayen takin don noma gonakan su.

“Matsalar ta fi shafar manoman da ke yin noma a karkara, inda samun takin ke ci gaba da kara zamar masu babbar matsala”.

“Shelanta cewa, sun samar da takin a cin farashi mai sauki, akasari idan aka bincika, magana ce kawai ta siyasa, amma ba a zahiri ba”.

Sun sanar da cewa, abin takaici yadda wasu `yan siyasa a kasar ke yin yakin neman zabe da takin don a zabe su, wanda da zaben ya wuce, takin zai kara yiwa manoman nisa.

Masanan sun kuma koka kan tasirin samar da takin, inda suka bayyana cewa, za fara damina a watan hudu, amma ba za a samun takin a kan lokaci, inda hakan ke sanya wa manoman ke fara yin noman a kan kurarren lokaci.

Har ila yau, sun sanar da cewa, ya zama wajibi mahukunta a fannin na samar da takin a kasar nan, su dinga baiwa manoman kasar, musamman kanana tallfi don su kara habaka sana’ar ta su ta noma da kuma samar wa da kansu da kudin shiga.

Cikas
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Abin Da Ya Sa Gwamnati Ta Kebe Wuraren Kiwo 368 Don Bunkasa Noma

Abin Da Ya Sa Gwamnati Ta Kebe Wuraren Kiwo 368 Don Bunkasa Noma

LABARAI MASU NASABA

Mutane 842 Ne Suka Rasa Ransu, Aka Yi Garkuwa Da Sama Da 270 A Watan Mayu – Rahoto

June 21, 2026
PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar  Jamiyyar

PRP Ta Zargi Kwankwaso Da Saye Fom Ɗin Takarar Jamiyyar

June 21, 2026
An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

An Ƙaddamar Da Dakarun Tsaron Daji 2,187 A Bauchi

June 21, 2026
An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

An Sanar Da Wadanda Suka Lashe Golden Goblet Na Bikin Fina-Finen Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 21, 2026
Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

Cibiyar CBA Ta Kenya Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da Wata Cibiyar Sin Wajen Bunkasa Noma Da Cinikayyar Lemar Kwadi

June 21, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

Kasar Sin Ta Karbi Bakuncin Taron Daidaita Batun Kare Hakkin Dan Adam

June 21, 2026
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi A Taron Majalissar UNHRC

June 21, 2026
Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

Ƴan Ta’adda Sun Ƙone Shingen Bincike Na NSCDC, Sun Sace Wani Mutum A Kebbi

June 21, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.