• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mamu Ya Dinga Kawo Cikas Ga Ceto Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna – Atta

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Mamu Ya Dinga Kawo Cikas Ga Ceto Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna – Atta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dokta AbdulMalik Atta, daya daga cikin kwamitin shugaban kasa da ya taimaka wajen ceto fasinjojin da aka sace daga jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a watan Maris, ya zargi mai yin sulhu da ‘yan ta’adda, Malam Tukur Mamu, da kawo cikas ga kokarin sako mutanen da aka sace. 

Atta, wanda mahaifinsa na cikin fasinjojin da aka sace, ya yi ikirari ne a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels.

  • Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina
  • Dalilinmu Na Yi Wa ASUU Kishiya –Gwamnati

Atta ya ce Mamu ya yi duk abin da zai iya domin dakile yunkurin gwamnatin tarayya na kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su domin amfanin kansa.

Ya ce, “Saboda kawo shawarar amfani da kudi da Mamu ya yi, ya sa iyalan wadanda abin ya shafa sun bayar da dala 200,000 kafin babban hafsan tsaron ya shiga tsakani.

“Kwamitin shugaban kasa ya yi namijin kokari saboda mun shiga dajin mu gana da ‘yan ta’addar har muka da su kwana a daji.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

“Yau watanni shida da mako guda kenan, amma mun gode wa Allah komai ya zo karshe a yanzu, sakamakon tallafin da gwamnatin tarayya ta samu ta ofishin babban hafsan sojin kasa. Mun iya shiga daji muka dawo da sauran ‘yan uwa.

“Mun cimma hakan ba ta hannun wani da ya ci amanar kwamitin da gwamnati ba, ina magana ne a kan Tukur Mamu wanda ya dinga dakile kokarin gwamnati don biyan bukatun kansa. Kamar yadda muka sani yanzu yana hannun gwamnati. Amma mun gode Allah, yanzu duk ’yan uwa sun kubuta.

“’Yan ta’addar ba su taba neman kudi a hannun kowa ba, amma Tukur Mamu ya dinga neman kudi a hannun iyalan wanda abun ya shafa ya kuma ya kawo cikas wajen ceto mutanen har na ysawo watanni shida da suka gabata.

“Mun yi asarar kusan Dalar Amurka 200,000. Alhamdulillah hafsan sojin kasa ya dauki nauyin komai da kafa kwamitin da bai taba tambayar kobo ba. Duk wata sadaukarwa da ake yi ya zuwa yanzu ya kasance na kashin kai ne don tabbatar da an sako wadanda abin ya shafa.

“A cikin kwamitin, zan iya tabbatar muku cewa na yi aiki tare da mutane masu dattako. Idan ina da dama, sai na an rabawa kowane lambar yabo. Mun yi kasada da rayukanmu, muka je daji, can muka kwana a cikin daji.

“Mun saurari koken wadancan mutane (’yan ta’adda), duk da mun san abin da suka yi ba daidai ba ne, amma dole mu ja su a jiki.

“Yana da kyau jami’an tsaro su sauya tsare-tsaren ayyukansu kuma ya kamata gwamnati ta kara bude kofa don jan kowa a jiki.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaAttaFasinjojin Jirgin Kasan Abuja-KadunaKwamitin Shugaban KasaTukur MamuYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina

Next Post

Ya Kashe Kaninsa Garin Gwajin Maganin Bindiga A Kwara

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

13 hours ago
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci
Manyan Labarai

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

18 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

23 hours ago
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
Manyan Labarai

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

24 hours ago
Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar
Manyan Labarai

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

1 day ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

1 day ago
Next Post
Ya Kashe Kaninsa Garin Gwajin Maganin Bindiga A Kwara

Ya Kashe Kaninsa Garin Gwajin Maganin Bindiga A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.