ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mamu Ya Dinga Kawo Cikas Ga Ceto Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna – Atta

by Sadiq
4 years ago
Mamu

Dokta AbdulMalik Atta, daya daga cikin kwamitin shugaban kasa da ya taimaka wajen ceto fasinjojin da aka sace daga jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a watan Maris, ya zargi mai yin sulhu da ‘yan ta’adda, Malam Tukur Mamu, da kawo cikas ga kokarin sako mutanen da aka sace. 

Atta, wanda mahaifinsa na cikin fasinjojin da aka sace, ya yi ikirari ne a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels.

  • Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina
  • Dalilinmu Na Yi Wa ASUU Kishiya –Gwamnati

Atta ya ce Mamu ya yi duk abin da zai iya domin dakile yunkurin gwamnatin tarayya na kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su domin amfanin kansa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Saboda kawo shawarar amfani da kudi da Mamu ya yi, ya sa iyalan wadanda abin ya shafa sun bayar da dala 200,000 kafin babban hafsan tsaron ya shiga tsakani.

“Kwamitin shugaban kasa ya yi namijin kokari saboda mun shiga dajin mu gana da ‘yan ta’addar har muka da su kwana a daji.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

“Yau watanni shida da mako guda kenan, amma mun gode wa Allah komai ya zo karshe a yanzu, sakamakon tallafin da gwamnatin tarayya ta samu ta ofishin babban hafsan sojin kasa. Mun iya shiga daji muka dawo da sauran ‘yan uwa.

“Mun cimma hakan ba ta hannun wani da ya ci amanar kwamitin da gwamnati ba, ina magana ne a kan Tukur Mamu wanda ya dinga dakile kokarin gwamnati don biyan bukatun kansa. Kamar yadda muka sani yanzu yana hannun gwamnati. Amma mun gode Allah, yanzu duk ’yan uwa sun kubuta.

“’Yan ta’addar ba su taba neman kudi a hannun kowa ba, amma Tukur Mamu ya dinga neman kudi a hannun iyalan wanda abun ya shafa ya kuma ya kawo cikas wajen ceto mutanen har na ysawo watanni shida da suka gabata.

“Mun yi asarar kusan Dalar Amurka 200,000. Alhamdulillah hafsan sojin kasa ya dauki nauyin komai da kafa kwamitin da bai taba tambayar kobo ba. Duk wata sadaukarwa da ake yi ya zuwa yanzu ya kasance na kashin kai ne don tabbatar da an sako wadanda abin ya shafa.

“A cikin kwamitin, zan iya tabbatar muku cewa na yi aiki tare da mutane masu dattako. Idan ina da dama, sai na an rabawa kowane lambar yabo. Mun yi kasada da rayukanmu, muka je daji, can muka kwana a cikin daji.

“Mun saurari koken wadancan mutane (’yan ta’adda), duk da mun san abin da suka yi ba daidai ba ne, amma dole mu ja su a jiki.

“Yana da kyau jami’an tsaro su sauya tsare-tsaren ayyukansu kuma ya kamata gwamnati ta kara bude kofa don jan kowa a jiki.”

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Ya Kashe Kaninsa Garin Gwajin Maganin Bindiga A Kwara

Ya Kashe Kaninsa Garin Gwajin Maganin Bindiga A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.