ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mamu Ya Dinga Kawo Cikas Ga Ceto Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna – Atta

by Sadiq
4 years ago
Mamu

Dokta AbdulMalik Atta, daya daga cikin kwamitin shugaban kasa da ya taimaka wajen ceto fasinjojin da aka sace daga jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a watan Maris, ya zargi mai yin sulhu da ‘yan ta’adda, Malam Tukur Mamu, da kawo cikas ga kokarin sako mutanen da aka sace. 

Atta, wanda mahaifinsa na cikin fasinjojin da aka sace, ya yi ikirari ne a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels.

  • Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina
  • Dalilinmu Na Yi Wa ASUU Kishiya –Gwamnati

Atta ya ce Mamu ya yi duk abin da zai iya domin dakile yunkurin gwamnatin tarayya na kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su domin amfanin kansa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Saboda kawo shawarar amfani da kudi da Mamu ya yi, ya sa iyalan wadanda abin ya shafa sun bayar da dala 200,000 kafin babban hafsan tsaron ya shiga tsakani.

“Kwamitin shugaban kasa ya yi namijin kokari saboda mun shiga dajin mu gana da ‘yan ta’addar har muka da su kwana a daji.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

“Yau watanni shida da mako guda kenan, amma mun gode wa Allah komai ya zo karshe a yanzu, sakamakon tallafin da gwamnatin tarayya ta samu ta ofishin babban hafsan sojin kasa. Mun iya shiga daji muka dawo da sauran ‘yan uwa.

“Mun cimma hakan ba ta hannun wani da ya ci amanar kwamitin da gwamnati ba, ina magana ne a kan Tukur Mamu wanda ya dinga dakile kokarin gwamnati don biyan bukatun kansa. Kamar yadda muka sani yanzu yana hannun gwamnati. Amma mun gode Allah, yanzu duk ’yan uwa sun kubuta.

“’Yan ta’addar ba su taba neman kudi a hannun kowa ba, amma Tukur Mamu ya dinga neman kudi a hannun iyalan wanda abun ya shafa ya kuma ya kawo cikas wajen ceto mutanen har na ysawo watanni shida da suka gabata.

“Mun yi asarar kusan Dalar Amurka 200,000. Alhamdulillah hafsan sojin kasa ya dauki nauyin komai da kafa kwamitin da bai taba tambayar kobo ba. Duk wata sadaukarwa da ake yi ya zuwa yanzu ya kasance na kashin kai ne don tabbatar da an sako wadanda abin ya shafa.

“A cikin kwamitin, zan iya tabbatar muku cewa na yi aiki tare da mutane masu dattako. Idan ina da dama, sai na an rabawa kowane lambar yabo. Mun yi kasada da rayukanmu, muka je daji, can muka kwana a cikin daji.

“Mun saurari koken wadancan mutane (’yan ta’adda), duk da mun san abin da suka yi ba daidai ba ne, amma dole mu ja su a jiki.

“Yana da kyau jami’an tsaro su sauya tsare-tsaren ayyukansu kuma ya kamata gwamnati ta kara bude kofa don jan kowa a jiki.”

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Ya Kashe Kaninsa Garin Gwajin Maganin Bindiga A Kwara

Ya Kashe Kaninsa Garin Gwajin Maganin Bindiga A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.