ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mamu Ya Dinga Kawo Cikas Ga Ceto Fasinjojin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna – Atta

by Sadiq
4 years ago
Mamu

Dokta AbdulMalik Atta, daya daga cikin kwamitin shugaban kasa da ya taimaka wajen ceto fasinjojin da aka sace daga jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a watan Maris, ya zargi mai yin sulhu da ‘yan ta’adda, Malam Tukur Mamu, da kawo cikas ga kokarin sako mutanen da aka sace. 

Atta, wanda mahaifinsa na cikin fasinjojin da aka sace, ya yi ikirari ne a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels.

  • Yadda Ta Kaya A Taron Gwamnonin Nijeriya Da Nijer A Katsina
  • Dalilinmu Na Yi Wa ASUU Kishiya –Gwamnati

Atta ya ce Mamu ya yi duk abin da zai iya domin dakile yunkurin gwamnatin tarayya na kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su domin amfanin kansa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Saboda kawo shawarar amfani da kudi da Mamu ya yi, ya sa iyalan wadanda abin ya shafa sun bayar da dala 200,000 kafin babban hafsan tsaron ya shiga tsakani.

“Kwamitin shugaban kasa ya yi namijin kokari saboda mun shiga dajin mu gana da ‘yan ta’addar har muka da su kwana a daji.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

“Yau watanni shida da mako guda kenan, amma mun gode wa Allah komai ya zo karshe a yanzu, sakamakon tallafin da gwamnatin tarayya ta samu ta ofishin babban hafsan sojin kasa. Mun iya shiga daji muka dawo da sauran ‘yan uwa.

“Mun cimma hakan ba ta hannun wani da ya ci amanar kwamitin da gwamnati ba, ina magana ne a kan Tukur Mamu wanda ya dinga dakile kokarin gwamnati don biyan bukatun kansa. Kamar yadda muka sani yanzu yana hannun gwamnati. Amma mun gode Allah, yanzu duk ’yan uwa sun kubuta.

“’Yan ta’addar ba su taba neman kudi a hannun kowa ba, amma Tukur Mamu ya dinga neman kudi a hannun iyalan wanda abun ya shafa ya kuma ya kawo cikas wajen ceto mutanen har na ysawo watanni shida da suka gabata.

“Mun yi asarar kusan Dalar Amurka 200,000. Alhamdulillah hafsan sojin kasa ya dauki nauyin komai da kafa kwamitin da bai taba tambayar kobo ba. Duk wata sadaukarwa da ake yi ya zuwa yanzu ya kasance na kashin kai ne don tabbatar da an sako wadanda abin ya shafa.

“A cikin kwamitin, zan iya tabbatar muku cewa na yi aiki tare da mutane masu dattako. Idan ina da dama, sai na an rabawa kowane lambar yabo. Mun yi kasada da rayukanmu, muka je daji, can muka kwana a cikin daji.

“Mun saurari koken wadancan mutane (’yan ta’adda), duk da mun san abin da suka yi ba daidai ba ne, amma dole mu ja su a jiki.

“Yana da kyau jami’an tsaro su sauya tsare-tsaren ayyukansu kuma ya kamata gwamnati ta kara bude kofa don jan kowa a jiki.”

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Next Post
Ya Kashe Kaninsa Garin Gwajin Maganin Bindiga A Kwara

Ya Kashe Kaninsa Garin Gwajin Maganin Bindiga A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.