ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

by Abubakar Abba
1 year ago
Hikimar

A ci gaba da yunkurin farfado da noman Filanten kimanin Kadada 6.5 a Jihar Nasarawa, wani kamfanin gidan gona mai suna ‘AA Dibine Agro’ da wata kungiyar manoma (COMAFAS), sun rattaba hannu tare kulla yarjejeniya; domin ci gaba da noman Filanten a fadin Jihar.

Isiaka Adamu Adamu, Manajan Darakta na Kamfanin ‘AA Dibine Agro Farm Limited’ da Dakta  Austine Maduka, wanda ya kafa kungiyar ta ‘COMAFAS’, sun amince da yarjejeniyar hadin gwiwar a lokacin da suka ziyarci gonar, don kulla dangantakar.

  • Sanusi II Ya Gudanar Da Hawan Nassarawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda A Kano
  • Kotu Ta Dakatar Da Yunkurin Aminu Ado Bayero Na Gyaran Fadar Nassarawa

Sun sanar da amincewar ne, a lokacin da suka kai ziyara kamfanin, inda a hukumance suka aminta da dangantar da kuma hadakar tasu.

ADVERTISEMENT

Wannan yarjejeniyar ta kasance a matsayin wani babban mataki na kara bunkasa noman na gonar, duba da irin dimbin albarkatun da ake da su, duk da cewa ana fuskantar karancin kudaden aiki, domin samar da kayan aikin da suka kamata da za a yi amfani da su wajen yin noman a gonar.

Dakta Maduka ya bayyana cewa, za kuma a samar da wasu karin wasu dabarun zamanin da za a yi aikin da su a gonar.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Gonar ta ‘AA Dibine Agro’, ta kasance a yankin Pasali Karshi da ke cikin karamar Hukumar Karu a Jihar Nasarawa.

Kazalika, kudirin shi ne; nomawa da kuma samar da isasshen Filanten din da za a rika kai wa har zuwa babban birnin tarayya  Abuja, domin sayar da shi.

A cewar tasa, abin da gonar ke son cimma shi ne, taimaka wa fannin aikin noma na tarayyar kasar nan, wanda hakan zai kuma kara tallafawa wajen kara samar da ayyukan yi ga ‘yan kasa tare da samar da wadataccen abinci.

Sai dai, ya bayyana cewa; rashin kudaden da za a yi amfani da su wajen cimma wannan manufa, su ne babban cikas.

Gonar, wadda aka samar da ita a zagayen Katangu, domin kiwon dabbobi, na matukar fama da karancin ruwa da ya yi sanadiyyar dakatar da gudanar da dukkanin wasu ayyuka da ake yi a cikinta.

Bugu da kari, rashin samar da hanya; wadda za a rika amfani da ita wajen safarar amfanin gonar da aka girbe, na daya daga cikin kalubalen da gonar ke fuskanta.

Amma duk da irin wadannan matsaloli da gonar ta ‘AA Dibine’ ke fuskanta, ta tanadi wasu muhimman manya-manyan shirye-shiye.

Daga cikin shirye-shiyen sun hada da; burin samar da wuraren kiwon dabbobi da kiwon Kajin gidan gona da wuraren kiwon Kifi da kuma sarrafa abincin dabbobi, wanda hakan zai taimaka wajen habaka tattalin arzikin yankin tare da samar da ayyukan yi da kuma kara bunkasa noma.

kungiyar ta COMAFAS, ta fi mayar da hankali ne wajen tallafa wa manoma da kuma kara habaka fannin aikin noma.

A cewar Dakta Maduka, kungiyar ta amince da yarjejeniyar ce, duba da cewa; ta lura da manufar da gonar ta ‘AA Dibine Farm Limited’, ta sanya a gaba, musamman domin tsamo gonar daga cikin babban kalubalen da take fuskanta tare kuma da samun damar cimma burin da ta sanya a gaba.

Ya kara da cewa, hadakar za kuma ta taimaka wajen samar da ilimi da masu zuba hannun jari da kuma samun tallafin kudi ga gonar. Haka zalika, kudin zai taimaka, wajen sama wa gonar kayan aikin da take bukata da kuma samar da hanyar yin jigilar amfanin gonar da aka shuka.

Sauran daukin da hadakar za ta samar, sun hada da horo da kuma tabbatar da shugabanci nagari da sauran makamantansu.

Dakta Maduka, ya kuma bayar ta tabbacin cewa; ta hanyar jawo sauran abokan hadaka cikin wannan aiki, za a iya noman wannan Filanten mai matukar tarin yawa a gonar, duba da cewa; yankin na da yanayi mai kyau na yin noma da ake bukata, inda kuma hakan zai kara taimakawa wajen samar da ayyukan yi.

Kazalika, ya bayyana cewa; hadakar za kuma ta kara taimakawa wajen kara habaka tattalin arzikin yankin tare da samar da wadataccen abinci yadda ya kamata. 

A cewar tasa, gonar ta ‘AA Dibine Farm Limited’, za ta kasance mai aiki da kayan noma na zamani a tsakanin sauran gonakin da ke fadin kasar nan, ta hanyar taimakon kungiyar ta COMAFAS.

Har ila yau, daukacin masu kulla wannan yarjejeniya, sun amince da kara habaka wannan bangare na noma a dukkanin fadin Nijeriya.

Hikimar
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran

Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman - Iran

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.