Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Yadda Matasa Miliyan Biyu Suka Rasa Aikin Yi Sakamakon Tsaida Rijistar Layuka

by Khalid Idris Doya
December 31, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Rijistar Layuka
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Sama da matasa ‘yan Nijeriya miliyan biyu ne suka kasance ‘yan zaman kashe-wando tun bayan dakatar da saidawa da rijistar layukan waya da gwamnatin Nijeriya ta yi ta hannun hukumar sadarwa.

Kungiyar dillalan layuka ta (ATOASDA) ita ce ta shaida hakan a ganawarta da ‘yan jarida a Kaduna.

samndaads

Dilolin layukan wadanda suka ce suna sane da kokarin gwamanti na yunkurin dakile matsalar tsaro da ake samu ta hanyar amfani da layukan sadarwa wanda suka kuduri aniyar hada bayanan layuka da lambar shaidar kasancewa dan kasa (NIN), amma kuma hakan ya jawo wa matasa sama da miliyan biyu kasancewa marasa aikin yi wanda hakan ma wani karin barazana ne.

Shugaban kungiyar ATOASDA na kasa, Hassan Yakubu ya yi bayanin cewa kungiyar tana da cikakken rijista da hukumar kula da kamfanoni ta kasa (CAC) wadanda mambobinsu suka kasance jami’an da ke taimaka kokarin gwamnatin tarayya na kare rayuka da dukiyar jama’a.

Ya ce, mafiya yawan wakilan saida layuka da sarrafa su sun kasance ne ‘yan shekaru 20 zuwa 40 da suke aikin rijista wa jama’a da kuma sabunta musu layukansu da aka dauka aikin hakan, wanda ya ce yanzu duk sun kasance kawai ‘yan zaman kashe wando.

Ya ce, suna lale da dukkanin wani tsare-tsare da shirye-shiryen gwamnati na tabbatar da tsaftace harkokin sadarwa, don haka ne ma suka yi fatan a samu nasarar kammala aikin hade lambobin bayanan layuka da na shaidar kasancewa dan kasa cikin kwanciyar hankali domin bada damar cimma manufofin da aka sanya a gaba.

Daga nan sun roki a bada damar a ci gaba da saida layuka da rijistar sabbi ko tsoffi domin jama’a su cigaba da samun aikin dogaro da kai a daukacin kananan hukumomi 774 da ke fadin kasar nan.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Dabara Ta Rage Ga Mai Shiga Rijiya

Next Post

Ina Da Yakinin APC Za Ta Sake Cin Zaben 2023 – Babangida Shinkafi

RelatedPosts

Marayu

’Yan Bindiga Sun Sace Marayu Bakwai A Gidan A Marayun Abuja

by Khalid Idris Doya
3 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Akwai dan dsoro na alamun tashin...

Bogi Wiwi

Legas: An Cafke Dan Sandan Bogi Da Wiwi

by Khalid Idris Doya
3 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Rahotanni daga Jihar Legas, sun zo...

Aguda

Mutum Ya Rasu A Arangamar Matasan Unguwar Aguda Dake Surulere

by Khalid Idris Doya
3 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, An tabbatar da mutuwar mutum daya...

Next Post
Babangida Shinkafi

Ina Da Yakinin APC Za Ta Sake Cin Zaben 2023 – Babangida Shinkafi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version