• English
  • Business News
Thursday, June 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mohammed Bello Koko Ya Tsaftace Hukumar Tashoshin Ruwan Nijeriya

by Bello Hamza
2 years ago
in Rahotonni
0
Yadda Mohammed Bello Koko Ya Tsaftace Hukumar Tashoshin Ruwan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kasa da shekara biyu a mastayinsa na shugaban Hukumar Tashoshin Ruwan Nijeriya NPA Mohammed Bello Koko ya samar da gaggarumin ci gaban da aka dade ba a samu irinsa ba.

Tashoshin ruwa na Nijeriya na ta dawo da kayan da aka yi hasararsu a baya ga kasashen da ake da makwabtaka da su sakamakon bunkasar ingantacciyar hanyar samar da kayayyaki, ingantacciyar yadda ake gudanar da zirga-zirgar ababen hawa, da saukin zirga-zirgar kayayyaki a tashoshin jiragen ruwa.

  • Tinubu Ya Shiga Wata Gana Wa Da Gwamnonin Jam’iyyar APC A Abuja

Kafin yanzu, an san tashar jiragen ruwa ta Nijeriya a matsayin daya daga cikin mafi tsada da rashin inganci a yankin Afirka ta Yamma da ta Tsakiya. Wannan ya sanya tashar ta kasance ba ta jan hankalin masu shigo da kaya ba, inda suka gwammace da su karkatar da kayayyakin da za su je Nijeriya zuwa tashoshin jiragen ruwa masu inganci a yankin.

Hakan ya faru ne saboda matsalolin da ke tattare da lalacewar kayayyakin jigila ta tashar jiragen ruwan, daukar dogon lokaci wajen dakon kaya, rashin ingancin jujjuyawar jirgin ruwan, daukar dogon lokaci wajen aikin sharer fage, da cunkoso da ke haifar da cunkoson ababen hawa a cikin tashar jiragen ruwan.

Wadannan kalubalen sun haifar da masu shigo da kaya na karkatar da kayayyakin zuwa kasashen makwabta, wanda hakan ya haifar da illa ga bunkasar hanyoyin kudaden shiga na kasa da kuma yadda ake sarrafa kayayyakin.

Labarai Masu Nasaba

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Sai dai al’amura sun fara daidaita, biyo bayan yunkurin da shugabancin hukumar NPA na yanzu ke yi na aiwatar da gyare-gyare tare da dawo da ka’ida a tashoshin jiragen ruwa.
An nada Bello-Koko a matsayin Manajan Darakta na hukumar a ranar 6 ga Mayu, 2021 a matsayin mukaddashi, sai dai an tabbatar da shi a ranar 21 ga Fabarairu, 2022. Tun daga wannan lokacin, tawagar Bello-Koko ta dukufa wajen sauya yadda lamura ke gudana.

A yanzu haka, tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya sun zama abin da aka fi so a yammacin Afirka, musamman ga kasashen da ba su da tudu kamar Jamhuriyar Nijar, wadanda ke nuna sha’awar jigilar kayansu daga Nijeriya.

Kammala tashar jiragen ruwa mai zurfi ta Lekki, daukar nauyin gyaran manyan titunan tashar jiragen ruwa da suka lalace, tare da kawo karshen cunkoso a tashoshin jiragen ruwa da kuma a hanyar tasoshin jiragen ruwan ta hanyar tabbatar amfani da na’urar kiran waya na daga cikin hanyoyin da hukumar ta ke samun nasarar tsaftace tashar jiragen ruwan.

Fiye da wannan, NPA a karkashin wannan shugabanci ta habbaka ayyuka a fannoni kamar:

Tara Kudade Zuwa Asusun Tarayya
Hukumar NPA karkashin Bello-Koko tana tallafawa tattalin arzikin kasa ta hanyar tara kudaden shiga da ba a taba ganin irinsa ba tare da turawa asusun hadakar kudaden shiga (CRF). Kudaden shiga na hukumar ya karu daga Naira biliyan 317 a shekarar 2020 zuwa Naira biliyan 361 a shekarar 2022, yayin da kudaden da ake aikawa da su ya karu daga Naira biliyan 80 a shekarar 2020 zuwa Naira biliyan 91 a shekarar 2022.

Binciken Businessday ya nuna cewa NPA a karkashin wannan jagorancin na yanzu ya nuna ta samar da sabbin sana’o’in da ba wai kawai sun samar wa ‘yan Nijeriya ayyukan yi ba, har ma sun kasance hanyoyin samun kudaden shiga.

Sun hada da samar da ayyukan jiragen ruwa, wanda baya ga rage matsi a titunan, ya kuma bunkasa har ya kai kasuwancin Naira biliyan 2, wanda hakan ya jawo jarin kai tsaye.
An yi bitar hauhawar hayan gidaje domin ya dace da halin da ake ciki na tattalin arziki da nufin inganta kudaden da hukumomi ke samu daga kula da kayyadaddun kadarorinta.

Har ila yau, ta ba da lasisin karin wuraren ajiya na manyan motoci domin kara karfin manyan motocin da ke aiki a tashoshin jiragen ruwa na Legas, da kuma bayar da lasisin guda 10 na Tashar fitarwa ta ‘Edport Processing Terminals (EPT)’ domin saukake fitar da kaya a tashar jiragen ruwa. Tashar ta samar da shagon tsayawa guda daya wanda ke ba da damar sarrafa inganci, tantance kaya daga dukkan hukumomin gwamnati, da kuma ba da izinin jigilar kayayyaki.
A yanzu, an sami gagarumin ci gaba ta fuskacin lokacin juyar da manyan motoci saboda nasarar aiwatar da tsarin kiran na zamani.

Domin tabbatar da bin tsarin kiran wayar, NPA ta tura babura 24 domin taimakawa wajen sa ido kan manyan motocin a mashigar Apapa/TCIPC/Ijora da kuma dorewar zirga-zirgar ababen hawa ba tare da cunkoso ba. Har ila yau, ta yi hadin gwiwa da jami’an ‘yan sanda domin katse shingayen binciken ababen hawa wadanda suke ba bisa ka’ida ba da ke kan hanyar tashar jiragen ruwa tare da kuma dakile cutar al’umma domin a samu nasarar tafiyar da ababen hawa cikin inganci.

Inganta Kayan Aikin Sintiri Da Kuma Tsaron Tashar Jiragen Ruwa
Hukumar NPA a karkashin Bello-Koko ta samar tare da girka ‘fairway buoys’ guda 86 a yankunan Warri da Calabar Pilotage domin ba da damar yin alamar tashoshi da taswirar hanya. Har ila yau, ta kuma samar da kananan jiragen ruwa, da suka hada da jiragen ruwa, ‘pilot cutters’, da jiragen sintiri, domin kawar da jinkirin da ke da nasaba da jigilar jiragen ruwa da tuki tare da bunkasa inganci. Har ila yau, ta sayo tare da tura kwale-kwale na jami’an tsaro zuwa dukkan gundumomin matukan jirgi domin magance hare-hare da ake kai wa jiragen ruwa a kan tashoshi da mashigin ruwa.

Habaka Kayayyakin Gudanarwa Da Kuma Ababen More Rayuwa
A cikin shekarar da ta gabata ne, jagorancin NPA ya kirkiro tashar siginar da za ta baiwa NPA damar ta kama motsin jiragen ruwa masu yawa. Har ila yau, an kammala binciken aikin wanke datti na barkewar hanyoyin ‘Escrabos’ domin kara karfin rike kwantena a tashar ruwan Ribers sakamakon sauya sararin da ba a yi amfani da shi ba a cikin tashar PTOL a tashar ruwan Ribers zuwa wurin da aka tattara.

Sauran sun hada da inganta ababen more rayuwa a tashar ‘B’, Berths 7 da kuma 8, da kuma tashar jiragen ruwa ta Onne ta hanyar hadin gwiwar gwamnati da kamfanuka masu zaman kansu (PPP) na gammayar kamfanin WACT Nigeria Limited wanda ya kai kimanin dala miliyan 110 a tsawon shekaru biyu. Wannan ya zuwa yanzu ya kai kashi 62 cikin dari na kammalawa.

Hukumar ta NPA ta kuma ba da izini ga gamayyar kamfanin Ringadars domin gina tankunan ‘bitumen metric’ mai daukar tan 6,000 a cikin tashar ruwa ta Ribers domin inganta karfin ajiyar ‘bitumen’ na kamfanin, wanda zai saukaka aiki tare da yin tasiri ga ci gaban ababen more rayuwa na Kudu maso Kudu. Ya zuwa yanzu dai an kammala aikin da kashi 58 cikin dari.

Jagorancin wannan hukumar a halin yanzu sun kasance a gaba wajen gwagwarmayar gyara abubuwan da suka lalace a tashar jiragen ruwa kuma sun kara samun amincewar gina katangar jinginar jiragen ruwa a mai lamba 15 a tashar jirgin ruwa ta Legas dake Apapa. Har ila yau, ta amince da kammala aikin hanyar zamani domin hadakar lamba ta 9, 10, da 11 a tashar jirgin ruwa ta Tarayya da ke tashar Onne.

Bello-Koko ya kuma samu amincewar sake gyara tasoshin kula da tashoshin jiragen ruwa na Legas da Tin-Can Island tare da samar da kuma sanya kariyar ruwa 180 domin inganta katangar kariya tare da kuma zama matakin riga-kafi domin dakile duk wani hatsari da ya taso daga jirgin ruwan kai tsaye zuwa katangar kariyar.

Hukumar ta NPA ta kammala ayyukan tuntubar juna domin kariya ga bakin ruwa da kuma gyara magudanar ruwa na Escrabos da kuma bincike da taswirar gundumar Warri Pilotage tun daga babbar titin Warri-Sapele har zuwa tashar Koko.

Tare da kaddamar da tashar ruwa mai zurfi ta Lekki cikin lokaci, NPA ta sami amincewar Majalisar Zartarwa ta Tarayya domin fara aikin gina tashar jiragen ruwa na Badagry, tare da kuma bayar da tallafi domin kafa tashoshin Ondo da Benin.

Kulla Alaka Da Bankin Duniya Da IFC
NPA ta sa Bankin Duniya da Hukumar Kula da Kudade ta Duniya domin ta samar da wata hanyar kudade domin bunkasa ababen more rayuwa ta tashar jiragen ruwa.

Ingantattun Bayanai Da Kuma ICT
Daya daga cikin abubuwan da ke kawo cikas ga ci gaba a fannin lura da tasoshin ruwa shi ne samun sahihan bayanai domin tsarawa. Sai dai tun bayan hawan Bello-Koko, shugabancinsa ta rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna da hukumar kididdiga ta kasa (NBS) domin nadar bayanai a zamanance domin musanya domin hada kididdigar tashoshin jiragen ruwa da kundin ajiye bayanai na kasa.

Shugaban NPA ya kuma sami sahhalewar domin bunkasa shafin Intanet na hukumar da kuma shafin Intanet na zirga-zirgar jiragen ruwan domin zama mai saukin amfani kuma domin sarrafa bayanai ta atomatik.

Hukumar ta kulla alakar aiki tare da Hukumar Kula da Ruwa ta Duniya (IMO), kan habaka tsarin tasoshin hukumar domin sarrafa ayyukan tashar jiragen ruwa a zamance.
Wannan ya biyo bayan bayar da kwangilar sabis na tuntuba domin lura da zirga-zirgar jiragen ruwa (BTS), ma’auni na aminci na lura da tasoshin ruwa wanda ke da damar wayarwa domin bai wa NPA damar samun jagora tare da samar da bayanan aminci ga jiragen ruwa a cikin tashoshin a bisa tsarin doka na kare rayuwa a tasoshin ruwa (SOLAS).

Jindadin Ma’aikata
A tarihi yake cewa Bello-Koko shi ne Babban Manajan Daraktan Hukumar na farko da ya tabbatar da ya samo amincewar karin albashin ma’aikata wanda ya tsaya cak a tsawon shekaru 15. Ya kuma kara da tabbatar da biyan kudaden fansho da kudaden ritaya ga wadanda suka yi ritaya cikin gaggawa.

Har ila yau, ya kuma tabbatar da karin girma ga ma’aikatan da suka cancanta cikin gaggawa tare da amsa bukatun kungiyoyin ma’aikatan tasoshin ruwa. Shugabancin hukumar NPA na yanzu ta gyara Cibiyar Horarwa ta Dockyard a Apapa domin ma’aikata, membobin tashar jiragen ruwa, da kuma kungiyoyin kamfanoni masu sha’awa. Mataki ne na rage kashe kudi wanda aka yi da nufin kula da albarkatu.

Ayyukan Taimakon Al’umma (CSR)
Ta fuskar CSR, shugaban hukumar NPA ya samar da ingantattun kayan wasanni da cikakken kayan aiki ga dukkanin makarantun firamare da sakandare na karamar hukumar Surulere da kewaye da ke amfani da su, tare da gyarawa da samar da kayan aiki ga babban asibitin karamar hukumar Apapa da kuma Bonny.

Har ila yau, ya samu saya tare da rarraba injunan dinki da nika domin karfafa al’ummomin da ke da kusa da tashar jiragen ruwa a Ribers, Calabar, da Warri domin habaka karfin kasuwanci a tsakanin kananan ‘yan kasuwa. Har ila yau, ya ci gaba da yin hulda tare da al’ummomin da suka karbi bakuncin tasoshin jiragen ruwan ta hanyar masu kula da tashar jiragen ruwa.

Bincike ya nuna cewa sauya fasali na hukumar da Bello-Koko ya soma ya samar wa da NPA nasarar lashe kyauta a mataki na 5 na ‘Platinum Lebel’ daga ofishin sake fasalin ma’aikatan gwamnati (BPSR) sakamakon samar da yanayi na samar da ayyuka masu inganci a kowane fanni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Next Post

Tinubu Ya Nada Akume Da Femi A Sakataren Gwamnati Da Shugaban Ma’aikatan Fadarsa

Related

jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

6 days ago
Bello Koko
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

2 weeks ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

2 weeks ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

3 weeks ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

3 weeks ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

4 weeks ago
Next Post
Tinubu Ya Nada Akume Da Femi A Sakataren Gwamnati Da Shugaban Ma’aikatan Fadarsa

Tinubu Ya Nada Akume Da Femi A Sakataren Gwamnati Da Shugaban Ma'aikatan Fadarsa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kai Farmaki Masana’antar Kera Bindiga, Sun Yi Kame A Taraba

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

June 19, 2025
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

June 19, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

June 19, 2025
Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Namadi Sambo Ya Karyata Sauya Sheƙa Zuwa APC

June 19, 2025
Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano

June 19, 2025
Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

Gwamnonin APC Sun Nemi Tinubu Ya Ƙirkiri ‘Yansandan Jihohi Don Yaƙar Matsalar Tsaro

June 19, 2025
Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

June 19, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama

Lakurawa Sun Sanya Dokar Hana Sayar Da Shanu A Kebbi

June 19, 2025
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya

June 18, 2025
Kawayen amarya

An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina

June 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.