• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko

Mun wallafa a Jaridarmu ta 12 ga Mayu, 2023

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Rahotonni
0
Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Masu sace mutane suna garkuwa da su domin neman kudin fansa na ci gaba da cin karensu ba babbaka bayan samun saukin lamarin lokacin gudanar da zabukan 2023.

Abin ya zama ruwan dare game duniya ta yadda hatta sarakuna iyayen kasa abin bai bar su ba, inda ‘yan bindigar ke ci gaba da keta alfarmarsu tare da na sauran ‘yan kasa masu bin doka da ba-su-ji-ba-ba-su-gani ba.

  • Gwamnan Katsina Ya Yi Wa Ma’aikatan Jihar Ƙarin ₦10,000 Kan Albashi, ‘Yan Fansho ₦5,000
  • Harin Filato: Gwamnati Ba Za Ta Huta Ba Har Sai An Hukunta Maharan – Shettima 

A ci gaba da kai hare-haren masu garkuwar, a farkon makon nan sun afka fadar Mai Martaba Sarkin Kagarko, Alhaji Sa’ad Abubakar mai shekara 103 a duniya, da ke unguwar Rimi, a Karamar Hukumar Kagarko da ke Jihar Kaduna, inda suka yi garkuwa da wasu daga cikin iyalinsa har mutum takwas.

Bugu da kari, bayan ‘yan bindigar sun fice daga gidansa ne kuma a kan hanyarsu ta fita daga garin suka sake yin awon gaba da wasu mutum hudu.

LEADERSHIP Hausa ta yi tattaki na musamman har zuwa fadar Mai Martaba Sarkin na Kagarko domin gano takamaimen abin da ya faru.

Mai martaba Sarkin wanda ya tarbi wakilinmu da hannu biyu-biyu, ya wakilta Galadiman Kagarko, Alhaji Sa’adu Sulaiman wanda har ila yau shi ne shugaban ma’aikata a fadar sarkin mai daraja ta biyu, ya yi mana bayanin abin da ya faru dalla-dalla.

Sarkin na zaune, Galadiman ya fara da bayanin cewa, lamarin ya faru ne a ranar 7 ga watan Mayun shekarar 2023 da misalin karfe 10 da rabi na dare, masu garkuwa da mutanen suka je gidan sarki bayan an yi ruwa an dauke.

“Sun shiga har dakinsa, da farko sun yi kokarin shiga ta kofar dakin, to ba su samu iko ba, sai suka fasa tagar dakin ta hanyar balle karafan tagar da gatura da kuma wasu karafa, amma ba su yi harbi da bindiga ba, sun same shi (sarkin) a daki tare da wasu ‘ya’yansa da jikokinsa wadanda suke tare da shi a wannan daren.

“Sun samu mai martaba a kan gadonsa, to, a lokacin da suke kokarin shigowa dakin, daya daga cikin ‘ya’yansa da ke cikin dakin da ya leka ya ga abin da ke faruwa, sai ya sanar da shi, sai sarki ya ce masa ya buya.

“Mutum na farko da ya shigo daga cikin barayin sai ya zauna a dakin ya ce (wa sarkin) ya bashi kudi, mai martaba ya nuna musu cewa ba shi da kudi. Ya ce da sarki kowane irin kudi ne in yana da shi ko Dalar Amurka ce ya bashi. Sarki ya ce to wa ya ce maka ina da kudi? Wanda ya ce maka ina da kudi ya zo ya dauka ya ba ka amma ni ba ni da kudi,” in ji mai magana da yawun sarkin.

Galadiman ya ci gaba da cewa, “dan bindigar ya ce wa sarki baba ba ka ga muna da bindiga ba? sarki ya ce bindiga ni ba ta ba ni tsoro, na san abin kashe mutane ce amma ni ba ta ba ni tsoro, don haka ni ba ni da kudi.

“Daga nan ne suka kyale sarkin, amma sauran ‘ya’ya da jokokin da suka samu suna kwance suna bacci a dakin duk sai suka tattara su suka tafi da su.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Akidar Siyasar Malam Aminu Kano Da Ta ‘Yan Siyasar Yanzu A Mizani –Farfesa Habu

Next Post

…Me Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ke Cikin Wahala Har Yanzu? 

Related

Kagarko
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

2 days ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 week ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 week ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
…Me Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ke Cikin Wahala Har Yanzu? 

…Me Ya Sa 'Yan Nijeriya Ke Cikin Wahala Har Yanzu? 

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.