ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko

Mun wallafa a Jaridarmu ta 12 ga Mayu, 2023

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Kagarko

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Masu sace mutane suna garkuwa da su domin neman kudin fansa na ci gaba da cin karensu ba babbaka bayan samun saukin lamarin lokacin gudanar da zabukan 2023.

Abin ya zama ruwan dare game duniya ta yadda hatta sarakuna iyayen kasa abin bai bar su ba, inda ‘yan bindigar ke ci gaba da keta alfarmarsu tare da na sauran ‘yan kasa masu bin doka da ba-su-ji-ba-ba-su-gani ba.

  • Gwamnan Katsina Ya Yi Wa Ma’aikatan Jihar Ƙarin ₦10,000 Kan Albashi, ‘Yan Fansho ₦5,000
  • Harin Filato: Gwamnati Ba Za Ta Huta Ba Har Sai An Hukunta Maharan – Shettima 

A ci gaba da kai hare-haren masu garkuwar, a farkon makon nan sun afka fadar Mai Martaba Sarkin Kagarko, Alhaji Sa’ad Abubakar mai shekara 103 a duniya, da ke unguwar Rimi, a Karamar Hukumar Kagarko da ke Jihar Kaduna, inda suka yi garkuwa da wasu daga cikin iyalinsa har mutum takwas.

Bugu da kari, bayan ‘yan bindigar sun fice daga gidansa ne kuma a kan hanyarsu ta fita daga garin suka sake yin awon gaba da wasu mutum hudu.

LEADERSHIP Hausa ta yi tattaki na musamman har zuwa fadar Mai Martaba Sarkin na Kagarko domin gano takamaimen abin da ya faru.

Mai martaba Sarkin wanda ya tarbi wakilinmu da hannu biyu-biyu, ya wakilta Galadiman Kagarko, Alhaji Sa’adu Sulaiman wanda har ila yau shi ne shugaban ma’aikata a fadar sarkin mai daraja ta biyu, ya yi mana bayanin abin da ya faru dalla-dalla.

Sarkin na zaune, Galadiman ya fara da bayanin cewa, lamarin ya faru ne a ranar 7 ga watan Mayun shekarar 2023 da misalin karfe 10 da rabi na dare, masu garkuwa da mutanen suka je gidan sarki bayan an yi ruwa an dauke.

“Sun shiga har dakinsa, da farko sun yi kokarin shiga ta kofar dakin, to ba su samu iko ba, sai suka fasa tagar dakin ta hanyar balle karafan tagar da gatura da kuma wasu karafa, amma ba su yi harbi da bindiga ba, sun same shi (sarkin) a daki tare da wasu ‘ya’yansa da jikokinsa wadanda suke tare da shi a wannan daren.

“Sun samu mai martaba a kan gadonsa, to, a lokacin da suke kokarin shigowa dakin, daya daga cikin ‘ya’yansa da ke cikin dakin da ya leka ya ga abin da ke faruwa, sai ya sanar da shi, sai sarki ya ce masa ya buya.

“Mutum na farko da ya shigo daga cikin barayin sai ya zauna a dakin ya ce (wa sarkin) ya bashi kudi, mai martaba ya nuna musu cewa ba shi da kudi. Ya ce da sarki kowane irin kudi ne in yana da shi ko Dalar Amurka ce ya bashi. Sarki ya ce to wa ya ce maka ina da kudi? Wanda ya ce maka ina da kudi ya zo ya dauka ya ba ka amma ni ba ni da kudi,” in ji mai magana da yawun sarkin.

Galadiman ya ci gaba da cewa, “dan bindigar ya ce wa sarki baba ba ka ga muna da bindiga ba? sarki ya ce bindiga ni ba ta ba ni tsoro, na san abin kashe mutane ce amma ni ba ta ba ni tsoro, don haka ni ba ni da kudi.

“Daga nan ne suka kyale sarkin, amma sauran ‘ya’ya da jokokin da suka samu suna kwance suna bacci a dakin duk sai suka tattara su suka tafi da su.”

Kagarko
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
…Me Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ke Cikin Wahala Har Yanzu? 

…Me Ya Sa 'Yan Nijeriya Ke Cikin Wahala Har Yanzu? 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.