ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Muka Yi Da ‘Yan Bindigar Da Suka Sace Iyalina – Sarkin Kagarko

Mun wallafa a Jaridarmu ta 12 ga Mayu, 2023

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Kagarko

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Masu sace mutane suna garkuwa da su domin neman kudin fansa na ci gaba da cin karensu ba babbaka bayan samun saukin lamarin lokacin gudanar da zabukan 2023.

Abin ya zama ruwan dare game duniya ta yadda hatta sarakuna iyayen kasa abin bai bar su ba, inda ‘yan bindigar ke ci gaba da keta alfarmarsu tare da na sauran ‘yan kasa masu bin doka da ba-su-ji-ba-ba-su-gani ba.

  • Gwamnan Katsina Ya Yi Wa Ma’aikatan Jihar Ƙarin ₦10,000 Kan Albashi, ‘Yan Fansho ₦5,000
  • Harin Filato: Gwamnati Ba Za Ta Huta Ba Har Sai An Hukunta Maharan – Shettima 

A ci gaba da kai hare-haren masu garkuwar, a farkon makon nan sun afka fadar Mai Martaba Sarkin Kagarko, Alhaji Sa’ad Abubakar mai shekara 103 a duniya, da ke unguwar Rimi, a Karamar Hukumar Kagarko da ke Jihar Kaduna, inda suka yi garkuwa da wasu daga cikin iyalinsa har mutum takwas.

Bugu da kari, bayan ‘yan bindigar sun fice daga gidansa ne kuma a kan hanyarsu ta fita daga garin suka sake yin awon gaba da wasu mutum hudu.

LEADERSHIP Hausa ta yi tattaki na musamman har zuwa fadar Mai Martaba Sarkin na Kagarko domin gano takamaimen abin da ya faru.

Mai martaba Sarkin wanda ya tarbi wakilinmu da hannu biyu-biyu, ya wakilta Galadiman Kagarko, Alhaji Sa’adu Sulaiman wanda har ila yau shi ne shugaban ma’aikata a fadar sarkin mai daraja ta biyu, ya yi mana bayanin abin da ya faru dalla-dalla.

Sarkin na zaune, Galadiman ya fara da bayanin cewa, lamarin ya faru ne a ranar 7 ga watan Mayun shekarar 2023 da misalin karfe 10 da rabi na dare, masu garkuwa da mutanen suka je gidan sarki bayan an yi ruwa an dauke.

“Sun shiga har dakinsa, da farko sun yi kokarin shiga ta kofar dakin, to ba su samu iko ba, sai suka fasa tagar dakin ta hanyar balle karafan tagar da gatura da kuma wasu karafa, amma ba su yi harbi da bindiga ba, sun same shi (sarkin) a daki tare da wasu ‘ya’yansa da jikokinsa wadanda suke tare da shi a wannan daren.

“Sun samu mai martaba a kan gadonsa, to, a lokacin da suke kokarin shigowa dakin, daya daga cikin ‘ya’yansa da ke cikin dakin da ya leka ya ga abin da ke faruwa, sai ya sanar da shi, sai sarki ya ce masa ya buya.

“Mutum na farko da ya shigo daga cikin barayin sai ya zauna a dakin ya ce (wa sarkin) ya bashi kudi, mai martaba ya nuna musu cewa ba shi da kudi. Ya ce da sarki kowane irin kudi ne in yana da shi ko Dalar Amurka ce ya bashi. Sarki ya ce to wa ya ce maka ina da kudi? Wanda ya ce maka ina da kudi ya zo ya dauka ya ba ka amma ni ba ni da kudi,” in ji mai magana da yawun sarkin.

Galadiman ya ci gaba da cewa, “dan bindigar ya ce wa sarki baba ba ka ga muna da bindiga ba? sarki ya ce bindiga ni ba ta ba ni tsoro, na san abin kashe mutane ce amma ni ba ta ba ni tsoro, don haka ni ba ni da kudi.

“Daga nan ne suka kyale sarkin, amma sauran ‘ya’ya da jokokin da suka samu suna kwance suna bacci a dakin duk sai suka tattara su suka tafi da su.”

Kagarko
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
…Me Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ke Cikin Wahala Har Yanzu? 

…Me Ya Sa 'Yan Nijeriya Ke Cikin Wahala Har Yanzu? 

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.