• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mutane Ke Tona Ramin Tururuwa Don Neman Abinci A Borno

by Sulaiman and Sadiq
9 months ago
in Labarai
0
Yadda Mutane Ke Tona Ramin Tururuwa Don Neman Abinci A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mata masu shayarwa da kananan yara a Jihar Borno, sun fara bin gidan tururuwa suna neman abinci, sakamakon ta’azzarar rashin abinci da karuwar cutar tamowa.

 

Mazauna wasu yankuna a Jihar Borno da ma’aikatan kiwon lafiya, sun shiga damuwa game da karuwar yara masu tamowa a jihar.

  • Girman Manzon Allah (SAW): Darasi Daga Suratul Fat’hi (I)
  • Matsalar Tsaro Da Hadurran Kwalekwale Da Ambaliyar Ruwa Na Cin Rayuka A Arewa

Abin da suka ce na da nasaba da rashin wadataccen abinci mai gina jiki ga mata masu shayarwa.

 

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Bugu da kari rahotanni sun nuna cewa kananan hukumomi bakwai ne a jihar Borno, matsalar ta fi shafa.

 

Kananan hukumomin sun hada da Marte da Kukawa da Abadam da Guzamala da Kaga da Mobar da kuma Gubio.

 

Yaran da ke a wadannan yankuna sun dogara ne da tallafin da suke samu daga kungiyoyin agaji.

 

Wata mata da ke aiki a kungiyoyin agaji, Fatima Muhammed Habib, ta manema labarai cewa, a da mutane ba su san ana fama da wannan matsala ba.

 

”Da muka je daya daga cikin wadannan yankuna mun tarar rabin yaran garin na fama da matsalar abinci mai gina jiki, haka suma matan da ke shayarwa, za ka gan su duk a wahale babu wani abinci mai maiko ko kyau da suke samu suna ci ga shi kuma suna shayarwa.”

 

Ta ce idan har uwa ba ta ci ta koshi ba ta yaya za ta samu ruwan nono bare har ta shayar da danta?

“Saboda tsananin yunwa haka za ka ga mata na tona gidan tururuwa don samu abinci, haka mata ke kungiya suna yawo don neman gidan tururuwar da za su samu abinci.”

 

“Babban abin tashin hankali shi ne daji matan ke zuwa don su samo gidan tururuwar, ga rashin tsaro a wuraren ga macizai da dai sauransu.” Ta ce suna kai musu taimako, amma taimakon ba lallai ya isa ba.

 

Yadda Lebura Ke Neman Abinci A Ramin Tururuwa A Bauchi

Idan ba a manta a Jihar Bauchi ma irin haka ta faru a watan Fabrairn 2024, inda leburori masu aikin karfi, suka koma tona gidan tururuwa domin neman abin da za su ci dangane da abin da suka kira na rashin ayyukan yi musamman tun daga lokacin da aka janye tallafin man fetur a Nijeriya.

 

Jaridar The Eagle-Eye Daily Post, ta ruwaito yadda ta taba cin karo da wani mutum mai aikin karfi mai suna Abubakar Salisu Na-giyade a Ibrahim Bako Bye-pass, inda ya hada zufa yana tona gidan tururuwa da nufin neman shinkafar da suka tara.

 

Leburan ya ce akwai ramin da ya samu kusan mudu biyu a ranar, yanzu kuma ya koma kan sabon rami wanda idan ya dace, zai iya hada mudu biyar idan aka gyara za a iya samun mudu biyu na shinkafar tuwo da kudinsu ya kai Naira 3,400 a wancan lokaci.

 

Ya ce a leburancin yini guda, ba ya wuce a biya mutum Naira 2,000 ko 3,000, shi ma aikin ba a cika samu a yanzu ba duba da yadda al’amura suka tsefe.

 

A cewarsa gyaran masai (shadda) ne, idan suka samu ake biyan ma’aikaci Naira 5,000 zuwa 10,000, wanda shi ka ya ce ba mutum daya ake bai wa kudin ba.

 

Leburan, ya ce yana da mata guda daya da yara takwas, ya kara da cewar dole ce ta sa ya fara aikin tona ramin tururuwa, tun da ya fahimci wani lokacin an fi samun abinci a wajen.

 

Kazalika, ya ce idan ya samo abinci a can sai dai kawai ya ji da na cefane ko kuma su bayar da shinkafar a ba su masara don su yi cefane kuma a haka suke rayuwa.

 

Ya ce yanzu haka, yana da ‘yan mata hudu wasu daga cikinsu sun kamala makarantun f6iramare da karamar Sakandare, amma rashin kudi ya sa suna zaune tare da su a gida sai Islamiyya da suke zuwa wanda malaman ko Naira 100 aka ba su suna hakuri.

 

A gefe guda leburan ya koka baya ga tsadar rayuwa, ya ce a gidan haya yake zaune ga kuma tsadar kudin sufuri, wanda hakan ya sa yake yin tafiyar kilomita mai tarin yawa da kafa don adana abin da ya samu a rana. Game da tallafin gwamnati da ake rabawa, ya ce ba su taba samun ko kwayar hatsi ba.

 

Fargabar Karuwa Cutar Tamowa A Arewacin Nijeriya

Ko a watan Yunin 2024, sa da kungiyar likitoci ta ‘Doctors Without Borders’ ta bayyana cewa an samu karuwar yara masu fama da tamowa a jihohi 11 da ke Arewacin Nijeriya da suka hada da Borno da Katsina da Sakkwato da Zamfara da Bauchi.

 

Kungiyar ta bayyana hakan a cikin rahotonta na 2024, inda ta ce an samu yara 1,250 a Jihar Borno kadai da ke fama da tamowa mai alaka da rashin abinci mai gina jiki, wanda ya ninka da kusan kashi dari a wasu yankunan, Arewa adadin da ya zarce na bara.

 

A cikin sanarwar da ta fitar MSF ta ce: “A cikin makonnin nan an samu gagarumar karuwar a yawan yara masu fama da mummunar cutar rashin isasshen abinci, wadda ke barazana ga rayuwarsu – wadanda ake kai wa asibitocin kungiyar”.

 

Ta kara da cewa wannan “abin tashin hankali ne idan aka yi kiyasin abin da zai faru lokacin da matsalar za ta kai matukarta a watan Yuli”.

 

Shugaban kungiyar ta MSF a Nijeriya, Dokta Simba Tirima ya ce: “Tun shekaru biyu da suka gabata muke ta gargadi game da yiwuwar mummunan rashin abinci mai gina jiki. Shekarun 2022 da 2023 sun kasance masu muni, amma abin da zai faru a 2024 ya fi muni”.

 

Jihohin da aka bayyana a matsayin wadanda matsalar ta fi shafa, akasarin su jihohi ne masu fama da matsalar tsaro.

 

Borno, inda abin ya fi kamari ta kwashe kusan shekara 15 tana fama da rikicin Boko Haram, lamarin da ya tagayyara kimanin mutum miliyan 2.5.

 

Wanna matsala ta yi tarnaki ga ayyukan noma da kiwo da harkar kasuwanci.

 

Mutane da dama sun zama ‘yan gudun hijira, inda aka samar da sansanonin tallafa wa ‘yan gudun hijira a fadin Arewa Maso Gabashin Nijeriya.

 

Tashin Farashin Kayayyaki

Tashin farashin kayayyaki, musamman na kayayyakin abinci a Nijeriya, ya tirsasa wa dubban ‘yan kasar komawa ga cin wasu nau’oin abincin da jama’a ba su saba da su ba.

 

A wasu yankuna an samu rahoton mutane kan fita daji inda suke ciro ciyawar ‘rai-ɗore’ suna dafawa sannan sun hada da kuli-kuli su ci domin maganin yunwa.

 

‘Yan Nijeriya dai suna ta korafi kan irin halin matsi da suka fada ciki, lamarin da ya sa iyalai da dama ba sa iya cin abinci kamar yadda ya kamata.

 

Sakamakon tsadar rayuwa, al’ummar jihohi da dama a Nijeriya suka yi ta gudanar da zanga-zangar neman dauki daga mahukunta.

 

Ya zuwa yanzu dai Gwamnatin Jihar Borno, karkashin jagorancin Babagana Umara Zulum ba ta ce komai kan lamarin ba, amma dai gwamnatin tana iya kokarinta wajen ganin ta tallafa wa masu rauni da wadanda rikicin Boko Haram ya rutsa da su.

 

Har wa yau, Zulum ya sha raba wa mutane da masu karamin karfi, kayan abinci da sauran kayan agaji da suke bukata.

 

A gefe guda kuma akwai kungiyoyin agaji masu tarin yawa da suke taimakawa da kayan agaji a jihar duk da cewar a wasu lokuta suna kokawa kan tallafin da suke samu na yin kadan.

 

Ko a watan Mayun 2024, sai da Majalisar Dinkin duniya da Gwamnatin Tarayya, suka yi kiran bukatar dala miliyan 306.4 domin magance matsalar tamowa a jihohin Borno da Adamawa da kuma Yobe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KuncinKuncin rayuwaTabarbarewar tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Girman Manzon Allah (SAW): Darasi Daga Suratul Fat’hi (I)

Next Post

An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

4 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

5 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

7 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

8 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

9 hours ago
Next Post
An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN

An Yi Watsi Da Ayyuka Na Fiye Da Naira Tiriliyan 17 A Nijeriya – Cibiyar CIPMN

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.