• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Yi Kicibis Da Labarin Mutuwata  -Jamila Janafty

by Leadership Hausa
2 years ago
in Nishadi
0
Yadda Na Yi Kicibis Da Labarin Mutuwata  -Jamila Janafty
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jamila Mamy Janafty, wacce sananniyar marubuciyar yanar gizo ce da ta wallafa littafan Hausa da dama da suka hada da SAIFUDDEEN, TA FITA ZAKKA, GIDANMU da dai sauransu.

Ta karyata rade-radin cewar Allah Ya yi mata rasuwa a ranar Asabar 11/03/2023. Zancen da ya mamaye duniyar rubutu da marubuta cikin kankanin lokaci kamar wutar daji.

  • ‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023
  • Kamata Ya Yi A Yi Hadin Kai Don Magance Kwayar Cutar COVID-19

Marubuciya Jamila, cikin wani gajeren rubutu da ta fitar dai, ta bayyana cewa: ba ma ita ba ce a hoton da ake yadawa da nufin ita ce,  asali ma ba ta da alaka da wannan hoton gaba daya.

Ga dai tattaunawar da wakilinmu ADAMU YUSUF INDABO ya yi da fitacciyar marubuciyar bayan da wasu suka kashe ta da fatar baki.

An ce kin mutu har an kai ki kushewa, to yanzu ke ce din ko fatalwarki ce nake magana da ita?

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

(Dariya) Ni ce nan da kaina ba fatalwa ba, saboda ina nan a raye ban mutu ba. Zuki ta malle ce kawai irin na masu son bayar da labari kuma ba su da abun fada, shi ne suke bigewa da kirkirar karyar cewa wai na mutu. Wanda hakan ba sabon abu ba ne kashe shahararrun mutane da baki, musamman fitattun jaruman fina-finai, da mawaka da kuma marubuta. To ni ma kusan abun da ya faru a kaina ke nan.

To ya kika ji da ana yada hotonki tare da cewar kin rasu?

Gaskiya ni ban ji komai ba, da farko Saboda ban dauka abun zai wuce tunanina ba. Ban zata abun zai yada duniya cikin lokaci kankani ba. Sannan karin abun da ya sa ban tashi hankalina ba shi ne, wannan hoton da suke yawo da shi, ba ni ba ce a cikin hoton. Asali ma ba ni da alaka da wannan hoton gaba daya.

Au hoton wacce aka lika a sanarwar mutuwar taki ke nan ba ke ba ce?

Ai kai ma ka san ba ni din ba ce. To na kara fada ma ni ma da bakina cewa ba ni ba ce, kuma ban san ta ba, ban san ina aka samo hoton ba. Yadda ka gan shi ni ma haka na gan shi.

Kuma ya kika fuskanci mutane da wannan al’amari?

Ai ranar da aka fara yada wannan labarin kanzon kuregen ban san wainar da ake toyawa ba, saboda wayata na kashe ta tun daran ranar da abun ya fara yaduwa. Sai da safe da misalin karfe Goma na safe (10:00AM) na kunna, sai ga wayar wata kawata marubuciya Surayyah Dahiru Gwaram ya fara shigo min tana sanar da ni ita ma ta samu kiran wayoyi ya fi a kirga a kan ana neman tabbacin na mutu ko ina nan da raina? Gaskiya ba ma ni ba hatta kawayena da makusantana sun sha kiran waya da amsa tambayoyin mutane a kan ko na mutun da gaske.

To wanna mataki kika dauka na shelantawa duniya cewar ke fa kina raye?

Na dauki matakin yin write-up gajere mai taken JANAFTY NA NAN A RAYE BA TA MUTU. Kuma na yi status da kaina a WhatsApp, kuma posting a dandalin abokai na facebook. Haka kuma na nemi ‘yan uwa da abokan arziki sun taya ni karyata wannan jita-jitar a shafukansu na yanar gizo. Ga kuma uwa uba wanannan tattaunawa da nake yi da jaridarku mai farin jini, da ita kadai ma ta isa gamsar da duniya cewa, Janafty numfashinta bai kare ba da saura.

Wacce rana abun ya fara yaduwa?

Ranar Asabar ne da yamma. (11/03/2023) saboda a ranar na samu labarin rasuwar daya daga cikin membes din cikin groups dina, sunanta Ummi Hafsah da ta yi hatsari kuma Allah ya yi mata rasuwa. Kuma ko hotonta ba mu fitar ba. To sai na bada sanarwan rasuwan nata a madadin duka members dina. Ina ga daga wannan lokacin ne sai aka sauya labari aka fara yawo da mutuwata,sannan labarin ya cigaba da bazuwa har yau din nan mutane suna ta kira da charts domin tabbatarwa.

To amma kin san shahararrun mutane dama an saba kashe su da baki. A ganin ki me ke kawo hakan?

To zan iya cewa kalubale daman na matakin nasara. Kuma daman ita nasara ba ta zuwa sai da kalubale. To ni dai ina nan da raina ban mutu ba . Wannan abun kuma da ya faru ba zai sauya komai ba, domin daman kowane mai rai wata rana mamaci ne. Sai dai na ce Alhamdulillah ina godiya ga Allah da kuma duka masoyana, na ga kauna, na gode kwarai. Allah ya bar zaman tare har gaban abada. Ameen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JaftyJAMILANishadi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Singapore: Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Hanya Ce Da Kasar Sin Ke Bi Wajen Taimakawa Ci Gaban Shiyyar Ta

Next Post

Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun

Related

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe
Nishadi

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

5 days ago
Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
Nishadi

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

2 weeks ago
Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda
Nishadi

Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda

2 weeks ago
Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri
Manyan Labarai

Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri

2 weeks ago
Jerin Manyan Jaruman Fim Da Nijeriya Ta Rasa A Yan Shekarun Nan
Nishadi

Jerin Manyan Jaruman Fim Da Nijeriya Ta Rasa A Yan Shekarun Nan

3 weeks ago
Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
Nishadi

Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?

4 weeks ago
Next Post
Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun

Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.