ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Na Yi Kicibis Da Labarin Mutuwata  -Jamila Janafty

by Leadership Hausa
3 years ago
Jamila

Jamila Mamy Janafty, wacce sananniyar marubuciyar yanar gizo ce da ta wallafa littafan Hausa da dama da suka hada da SAIFUDDEEN, TA FITA ZAKKA, GIDANMU da dai sauransu.

Ta karyata rade-radin cewar Allah Ya yi mata rasuwa a ranar Asabar 11/03/2023. Zancen da ya mamaye duniyar rubutu da marubuta cikin kankanin lokaci kamar wutar daji.

  • ‘Yan Nijeriya Sama Da Mutane 39 Ne Suka Mutu A Zaben 2023
  • Kamata Ya Yi A Yi Hadin Kai Don Magance Kwayar Cutar COVID-19

Marubuciya Jamila, cikin wani gajeren rubutu da ta fitar dai, ta bayyana cewa: ba ma ita ba ce a hoton da ake yadawa da nufin ita ce,  asali ma ba ta da alaka da wannan hoton gaba daya.

ADVERTISEMENT

Ga dai tattaunawar da wakilinmu ADAMU YUSUF INDABO ya yi da fitacciyar marubuciyar bayan da wasu suka kashe ta da fatar baki.

An ce kin mutu har an kai ki kushewa, to yanzu ke ce din ko fatalwarki ce nake magana da ita?

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

(Dariya) Ni ce nan da kaina ba fatalwa ba, saboda ina nan a raye ban mutu ba. Zuki ta malle ce kawai irin na masu son bayar da labari kuma ba su da abun fada, shi ne suke bigewa da kirkirar karyar cewa wai na mutu. Wanda hakan ba sabon abu ba ne kashe shahararrun mutane da baki, musamman fitattun jaruman fina-finai, da mawaka da kuma marubuta. To ni ma kusan abun da ya faru a kaina ke nan.

To ya kika ji da ana yada hotonki tare da cewar kin rasu?

Gaskiya ni ban ji komai ba, da farko Saboda ban dauka abun zai wuce tunanina ba. Ban zata abun zai yada duniya cikin lokaci kankani ba. Sannan karin abun da ya sa ban tashi hankalina ba shi ne, wannan hoton da suke yawo da shi, ba ni ba ce a cikin hoton. Asali ma ba ni da alaka da wannan hoton gaba daya.

Au hoton wacce aka lika a sanarwar mutuwar taki ke nan ba ke ba ce?

Ai kai ma ka san ba ni din ba ce. To na kara fada ma ni ma da bakina cewa ba ni ba ce, kuma ban san ta ba, ban san ina aka samo hoton ba. Yadda ka gan shi ni ma haka na gan shi.

Kuma ya kika fuskanci mutane da wannan al’amari?

Ai ranar da aka fara yada wannan labarin kanzon kuregen ban san wainar da ake toyawa ba, saboda wayata na kashe ta tun daran ranar da abun ya fara yaduwa. Sai da safe da misalin karfe Goma na safe (10:00AM) na kunna, sai ga wayar wata kawata marubuciya Surayyah Dahiru Gwaram ya fara shigo min tana sanar da ni ita ma ta samu kiran wayoyi ya fi a kirga a kan ana neman tabbacin na mutu ko ina nan da raina? Gaskiya ba ma ni ba hatta kawayena da makusantana sun sha kiran waya da amsa tambayoyin mutane a kan ko na mutun da gaske.

To wanna mataki kika dauka na shelantawa duniya cewar ke fa kina raye?

Na dauki matakin yin write-up gajere mai taken JANAFTY NA NAN A RAYE BA TA MUTU. Kuma na yi status da kaina a WhatsApp, kuma posting a dandalin abokai na facebook. Haka kuma na nemi ‘yan uwa da abokan arziki sun taya ni karyata wannan jita-jitar a shafukansu na yanar gizo. Ga kuma uwa uba wanannan tattaunawa da nake yi da jaridarku mai farin jini, da ita kadai ma ta isa gamsar da duniya cewa, Janafty numfashinta bai kare ba da saura.

Wacce rana abun ya fara yaduwa?

Ranar Asabar ne da yamma. (11/03/2023) saboda a ranar na samu labarin rasuwar daya daga cikin membes din cikin groups dina, sunanta Ummi Hafsah da ta yi hatsari kuma Allah ya yi mata rasuwa. Kuma ko hotonta ba mu fitar ba. To sai na bada sanarwan rasuwan nata a madadin duka members dina. Ina ga daga wannan lokacin ne sai aka sauya labari aka fara yawo da mutuwata,sannan labarin ya cigaba da bazuwa har yau din nan mutane suna ta kira da charts domin tabbatarwa.

To amma kin san shahararrun mutane dama an saba kashe su da baki. A ganin ki me ke kawo hakan?

To zan iya cewa kalubale daman na matakin nasara. Kuma daman ita nasara ba ta zuwa sai da kalubale. To ni dai ina nan da raina ban mutu ba . Wannan abun kuma da ya faru ba zai sauya komai ba, domin daman kowane mai rai wata rana mamaci ne. Sai dai na ce Alhamdulillah ina godiya ga Allah da kuma duka masoyana, na ga kauna, na gode kwarai. Allah ya bar zaman tare har gaban abada. Ameen.

Jamila
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
Nishadi

Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Nishadi

Ya Kamata Mawaƙa Su Guji Munafunci Da Hassada Su Rungumi Juna —Fati UK

May 23, 2026
Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano
Nishadi

Har Yanzu Burina Bai Cika Ba A Waka —Hadiza Maikano

May 16, 2026
Next Post
Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun

Wani Mutum Ya Yi Wa ‘Yarsa Ciki, Ya Yi Barazanar Kashe Ta A Ogun

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.