Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Yadda Na Zana Taswirar Kasuwar Sabon Garin Kano -Alin Bagadaza

by Tayo Adelaja
September 19, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kano

A cikin makon da ya gabata ne shugaban kungiyar ‘yan Kasuwar Sabon Gari a Jihar Kano, Alhaji Ali Bagadaza ya bayyana yadda aka tsara ginin kasuwar.

samndaads

Ya ce, a lokacin mulkin Soja na Janar Sani Abacha, lokacin da Wase yake a matsayin Gwamna a Kano, wannan lokacin ya kira shi akan a tsara ginin Kasuwar Sabon Gari. “Farar takarda kawai aka bani na zana taswirar da a halin yanzu kasuwar ke kanta”. In ji Alin Bagadaza

Shugaban yayi wannan bayani ne a lokacin da Majalisar Matasan Arewa masu kishin zaman lafiya ta karrama shi da lambar Ambasadan zaman lafiya a Kano.

Ya bukaci kwamitin da aka dorawa alhakin tattara gudummawar taimakon wadanda annobar gobara ta rutsa da su a kasuwanni daban-daban a Jihar Kano da cewa lallai a tabbatar da fito da wadannan kudade a raba.

Alin Bagadaza ya jadadda godiyarsa ga wannan majalisar matasa bisa hangen nesan da su ka yi na bashi wannan lambar yabo, ya ce; za mu ci gaba da yin abin da ya kamata domin ‘yan baya su kwaikwaya.

Shi ma da yake gabatar da na sa Jawabin shugaban kungiyar Majalisar matasan Arewar masu kishin zaman lafiya, Kwamared Yakubu Usaini Takai ya bayyana cewa akwai ka’idojin da kungiyar ke bi domin zakulo wanda za a karrama da wannan lambar ta ‘Ambasadan Zaman lafiya’, ya ce, “ciki akwai sharadin cewa dole wanda za a ba lambar ya kasance dattijon arziki ne wanda ba a samunsa cikin rikita-rikitar kudade, kuma ya kasance amintacce ta fuskar Jama’a, zakakuri wajen kishin ci gaban sana’ar da ya ke, wannan tasa muka zabi baiwa Alhaji Ali Bagadaza da wasu fitattun mutane wannan lamba ta Ambasadan zaman lafiya.”

Kungiyoyi, shuwagabannin al’umma, ‘yan Kasuwa da abokan arziki ne suka yi dafifi a otal din Royar inda aka gudanar da wannan babban taro.

SendShareTweetShare
Previous Post

Za Mu Yi Tsayin Daka Har Sai An Inganta Ilimin Mata Da Yara A Bauchi -Hajiya Suwaiba

Next Post

Ya Kamata A Kafa Kwamitin Binciko Wadanda Suka Kashe Shugaba ‘Yar Aduwa -Sanata Shehu Sani

RelatedPosts

Kawuna

Kawuna Ya Turo Ni Kano Don Yin Garkuwa Da Mutane, In Ji Maryam  

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Maryam Muhammad, wadda ta shahara wajen...

Beli

Ka Sake Ba Ni Beli – Maina Ga Alkali

by Muhammad
3 days ago
0

Ya Ce, Da Gaske Ba Shi Da Lafiya Daga Khalid...

Bude Makarantu

Korona: Ba Ja Baya Ga Bude Makarantu – Gwamnatin Bauchi

by Muhammad
2 weeks ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Bauchi ta...

Next Post

Ya Kamata A Kafa Kwamitin Binciko Wadanda Suka Kashe Shugaba ‘Yar Aduwa -Sanata Shehu Sani

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version