• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sabon Irin ‘Tela Maize’ Zai Rage Asarar Da Manoman Masara Ke Yi

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Yadda Sabon Irin ‘Tela Maize’ Zai Rage Asarar Da Manoman Masara Ke Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Manoman Masara a Nijeriya suna gab da farfadowa daga irin asarar da suke tafkawa sakamakon barnar da kwari da kuma karancin ruwa da suke fuskanta a duk shekara, an kiyarsata asarar da ke yi ya kai na fiye da Naira Biliyan 9, wannan na faruwa ne sakamakon sabin irin masara na ‘Tela Maize’ da Cibiyar Binciken Harkokin Noma (IAR) da ke karkashin Jami’ar Ahmadu Bello Zariya ta samar ana kuma gab da fara gabatar dashi Manoman kasar nan.

A kasar da ke da mutane fiye da Miliyan 200 ana kuma samar da Tan Miliyan 12 na masara maimakon Tan Miliyan 18 na masara da ke bukata, a kan haka ake shigo da ragowa Tan miliyan 6 don cike gibin da ake bukata domin amfani a cikin gida.

  • 2023: Wasu Sun Yanki Fom Din Takara Na Miliyan 100 Don Fakewa Da Neman Minista —Okorocha

Baya ga dogaro da shigo da kayan abinci daga kasashen waje matsalolin sauyin yanayi ya sanya ana noma Tan 2.5 zuwa Tan 3 a hecta; tabbas wannan ya yi matukar karanci hakan kuma na daga cikin matsalolin da ke haifar da karancin abinci a wannan lokacin.

A jawabinsa a gonar gwaji na ‘TELA Maize’ da aka yi a karamar hukumar Minjibir ta Jihar Kano a makon jiya, Shugaban Cibiyar Binciken Aikin Noma (IAR) Zariya, Farfesa Mohammad Ishiyaku, ya bayyana cewa, an samar da sabon irin masara na ‘Tela Maize’ ta yadda zai iya jure farmakin kwari da kuma karancin ruwa, a halin yanzu manoma na tsimin fiye da Dala Biliyan 9 (Dala Miliyan 24) a duk shekara wajen magunguna kashe kari da suke saya don yin feshin kadadan fili noma da ya kai hekta 500.
Ya kuma kara da cewa, daga cikin Naira Biliyan 9 da aka kiyasta za a samu manoma za su yi tsimin Naira Biliyan 3 da ake kashewa wajen feshin kadada 500 za kuma a yi tsimin fiye da Naira Biliyan 6 na asarar da ke yi sakamakon illar rashin ruwa a duk shekara.
Farfesa Ishiyaku ya bayyana cewa, IAR ta samu gaggaruwa nasara a fannoni da fama tun da aka fara binciken samar da irin ‘TELA Maize’ musamman a kan gonakin gwaji da aka kafa a sassan kasar inda aka fahimci yadda irin ke iya jure wa fari da farmakin kwari. Ya ce, wadannan nasarorin za su taimaka wajen warware matsalolin da manoma ke fuskanta tare da bunkasa tattalin arzikin kasa wanda zai kai Nijeriya ga dogaro da kai a wajen samar da abinci ga ‘yan kasa.
Ya kuma bayyana cewa, a tsawon shekara 100 da kafa Cibiyar Binciken Harkokin Noma (IAR) na Samaru ta gudabar da bincike da dama a kan kayyakin noma daban-daban wadanda suka kai ga kara yabanyar da manoma ke samu da kuma bunkasa tattalin arzikinsu gaba daya.
A nashi jawabin, shugaban kwamitin samar da irin ‘TELA Maize’ a Nijeriya, Farfesa Rabiu Adamu, ya ce,an fara bincike don samar da irin a Nijeriya ne tun a shekarar 2019 an kuma yi haka ne saboda matsalolin da kwarin ‘Fall armyworm’ da ‘Stem-borers’ ke haifarwa a kan masara wanda hakan ke janyo asarar fiye kashi 80 na masarar da ake nomawa a fadin kasar nan.
Farfesa Rabiu Adamu wanda masani ne a bangaren kwari da yadda suke barnata shuka, ‘Entomology’, ya ce, samar da irin ‘TELA Maize’, zai taimaka wajen rage yadda manoma ke amfani da magunguna kashe kwari wanda hakan zai takaita yadda amfanin dasu ke cutar da muhalli da rayuwar al’umma. Ya ce, samar da ‘Tela Maize aiki ne na wata hadaka data hada da Gidauniyar Inganta Aikin Gona ta Afrika (AATF) a kasasshen Afrika 7 wanda suka hada da Kenya, Uganda, Tanzania, Ethiopia, Mozambikue, Nijeriya da kuma Afrika ta Kudu.
Manoman sun yi maraba tare da nuna jin dadinsu a kan samar da ‘Tela Maize’ wanda suka ce, tabbass zai bunkasa harkar noma a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS

Next Post

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Bishiyar Dogon-yaro

Related

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

5 days ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

5 days ago
Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

6 days ago
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje
Noma Da Kiwo

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

2 weeks ago
Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

2 weeks ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

3 weeks ago
Next Post
Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Bishiyar Dogon-yaro

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Bishiyar Dogon-yaro

LABARAI MASU NASABA

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

August 14, 2025
Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

Sashen Aikewa Da Kunshin Sakwanni Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni 7 Na Farkon Bana

August 14, 2025
Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe

August 14, 2025
Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

August 14, 2025
Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

Gwamnati Na Ƙoƙarin Tsoratar Da Ni Don In Shiga APC – Sanata Tambuwal

August 14, 2025
Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Masana’antar Lantarki Ya Ci Gaba Da Samun Karfin Juriya A Kasar Sin

August 14, 2025
Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

Gidauniya Ta Rabar Da Buhun Takin Zamani 6,000 Ga Manoma A Bauchi 

August 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Kama Mutane 107 Da Ake Zargi, Sun Ceto Mutane 20 A Cikin Mako Guda – DHQ

August 14, 2025
‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Za Su Gudanar Da Zagaye Na 3 Na Aiki A Wajen Cibiyar Binciken Sararin Samaniya Ta Sin

August 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Kama Wani Mai Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Wani Yaro Ɗan shekara 2 A Yobe

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.