• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sabon Irin ‘Tela Maize’ Zai Rage Asarar Da Manoman Masara Ke Yi

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Yadda Sabon Irin ‘Tela Maize’ Zai Rage Asarar Da Manoman Masara Ke Yi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

Manoman Masara a Nijeriya suna gab da farfadowa daga irin asarar da suke tafkawa sakamakon barnar da kwari da kuma karancin ruwa da suke fuskanta a duk shekara, an kiyarsata asarar da ke yi ya kai na fiye da Naira Biliyan 9, wannan na faruwa ne sakamakon sabin irin masara na ‘Tela Maize’ da Cibiyar Binciken Harkokin Noma (IAR) da ke karkashin Jami’ar Ahmadu Bello Zariya ta samar ana kuma gab da fara gabatar dashi Manoman kasar nan.

A kasar da ke da mutane fiye da Miliyan 200 ana kuma samar da Tan Miliyan 12 na masara maimakon Tan Miliyan 18 na masara da ke bukata, a kan haka ake shigo da ragowa Tan miliyan 6 don cike gibin da ake bukata domin amfani a cikin gida.

  • 2023: Wasu Sun Yanki Fom Din Takara Na Miliyan 100 Don Fakewa Da Neman Minista —Okorocha

Baya ga dogaro da shigo da kayan abinci daga kasashen waje matsalolin sauyin yanayi ya sanya ana noma Tan 2.5 zuwa Tan 3 a hecta; tabbas wannan ya yi matukar karanci hakan kuma na daga cikin matsalolin da ke haifar da karancin abinci a wannan lokacin.

A jawabinsa a gonar gwaji na ‘TELA Maize’ da aka yi a karamar hukumar Minjibir ta Jihar Kano a makon jiya, Shugaban Cibiyar Binciken Aikin Noma (IAR) Zariya, Farfesa Mohammad Ishiyaku, ya bayyana cewa, an samar da sabon irin masara na ‘Tela Maize’ ta yadda zai iya jure farmakin kwari da kuma karancin ruwa, a halin yanzu manoma na tsimin fiye da Dala Biliyan 9 (Dala Miliyan 24) a duk shekara wajen magunguna kashe kari da suke saya don yin feshin kadadan fili noma da ya kai hekta 500.
Ya kuma kara da cewa, daga cikin Naira Biliyan 9 da aka kiyasta za a samu manoma za su yi tsimin Naira Biliyan 3 da ake kashewa wajen feshin kadada 500 za kuma a yi tsimin fiye da Naira Biliyan 6 na asarar da ke yi sakamakon illar rashin ruwa a duk shekara.
Farfesa Ishiyaku ya bayyana cewa, IAR ta samu gaggaruwa nasara a fannoni da fama tun da aka fara binciken samar da irin ‘TELA Maize’ musamman a kan gonakin gwaji da aka kafa a sassan kasar inda aka fahimci yadda irin ke iya jure wa fari da farmakin kwari. Ya ce, wadannan nasarorin za su taimaka wajen warware matsalolin da manoma ke fuskanta tare da bunkasa tattalin arzikin kasa wanda zai kai Nijeriya ga dogaro da kai a wajen samar da abinci ga ‘yan kasa.
Ya kuma bayyana cewa, a tsawon shekara 100 da kafa Cibiyar Binciken Harkokin Noma (IAR) na Samaru ta gudabar da bincike da dama a kan kayyakin noma daban-daban wadanda suka kai ga kara yabanyar da manoma ke samu da kuma bunkasa tattalin arzikinsu gaba daya.
A nashi jawabin, shugaban kwamitin samar da irin ‘TELA Maize’ a Nijeriya, Farfesa Rabiu Adamu, ya ce,an fara bincike don samar da irin a Nijeriya ne tun a shekarar 2019 an kuma yi haka ne saboda matsalolin da kwarin ‘Fall armyworm’ da ‘Stem-borers’ ke haifarwa a kan masara wanda hakan ke janyo asarar fiye kashi 80 na masarar da ake nomawa a fadin kasar nan.
Farfesa Rabiu Adamu wanda masani ne a bangaren kwari da yadda suke barnata shuka, ‘Entomology’, ya ce, samar da irin ‘TELA Maize’, zai taimaka wajen rage yadda manoma ke amfani da magunguna kashe kwari wanda hakan zai takaita yadda amfanin dasu ke cutar da muhalli da rayuwar al’umma. Ya ce, samar da ‘Tela Maize aiki ne na wata hadaka data hada da Gidauniyar Inganta Aikin Gona ta Afrika (AATF) a kasasshen Afrika 7 wanda suka hada da Kenya, Uganda, Tanzania, Ethiopia, Mozambikue, Nijeriya da kuma Afrika ta Kudu.
Manoman sun yi maraba tare da nuna jin dadinsu a kan samar da ‘Tela Maize’ wanda suka ce, tabbass zai bunkasa harkar noma a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS

Next Post

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Bishiyar Dogon-yaro

Related

Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

6 days ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

6 days ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

3 weeks ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Bishiyar Dogon-yaro

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Bishiyar Dogon-yaro

LABARAI MASU NASABA

majalisar kasa

‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8

July 25, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Mene Ne Birnin Zamani Na Al’umma

Fahimtar Sabon Tunani: Mene Ne Birnin Zamani Na Al’umma

July 25, 2025
Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

July 25, 2025
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

July 25, 2025
Amcon

Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi

July 25, 2025
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

July 25, 2025

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

July 25, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

July 25, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma

July 25, 2025
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.