ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sabon Irin ‘Tela Maize’ Zai Rage Asarar Da Manoman Masara Ke Yi

by Abubakar Abba
4 years ago
Tela Maize

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Manoman Masara a Nijeriya suna gab da farfadowa daga irin asarar da suke tafkawa sakamakon barnar da kwari da kuma karancin ruwa da suke fuskanta a duk shekara, an kiyarsata asarar da ke yi ya kai na fiye da Naira Biliyan 9, wannan na faruwa ne sakamakon sabin irin masara na ‘Tela Maize’ da Cibiyar Binciken Harkokin Noma (IAR) da ke karkashin Jami’ar Ahmadu Bello Zariya ta samar ana kuma gab da fara gabatar dashi Manoman kasar nan.

A kasar da ke da mutane fiye da Miliyan 200 ana kuma samar da Tan Miliyan 12 na masara maimakon Tan Miliyan 18 na masara da ke bukata, a kan haka ake shigo da ragowa Tan miliyan 6 don cike gibin da ake bukata domin amfani a cikin gida.

  • 2023: Wasu Sun Yanki Fom Din Takara Na Miliyan 100 Don Fakewa Da Neman Minista —Okorocha

Baya ga dogaro da shigo da kayan abinci daga kasashen waje matsalolin sauyin yanayi ya sanya ana noma Tan 2.5 zuwa Tan 3 a hecta; tabbas wannan ya yi matukar karanci hakan kuma na daga cikin matsalolin da ke haifar da karancin abinci a wannan lokacin.

ADVERTISEMENT

A jawabinsa a gonar gwaji na ‘TELA Maize’ da aka yi a karamar hukumar Minjibir ta Jihar Kano a makon jiya, Shugaban Cibiyar Binciken Aikin Noma (IAR) Zariya, Farfesa Mohammad Ishiyaku, ya bayyana cewa, an samar da sabon irin masara na ‘Tela Maize’ ta yadda zai iya jure farmakin kwari da kuma karancin ruwa, a halin yanzu manoma na tsimin fiye da Dala Biliyan 9 (Dala Miliyan 24) a duk shekara wajen magunguna kashe kari da suke saya don yin feshin kadadan fili noma da ya kai hekta 500.
Ya kuma kara da cewa, daga cikin Naira Biliyan 9 da aka kiyasta za a samu manoma za su yi tsimin Naira Biliyan 3 da ake kashewa wajen feshin kadada 500 za kuma a yi tsimin fiye da Naira Biliyan 6 na asarar da ke yi sakamakon illar rashin ruwa a duk shekara.
Farfesa Ishiyaku ya bayyana cewa, IAR ta samu gaggaruwa nasara a fannoni da fama tun da aka fara binciken samar da irin ‘TELA Maize’ musamman a kan gonakin gwaji da aka kafa a sassan kasar inda aka fahimci yadda irin ke iya jure wa fari da farmakin kwari. Ya ce, wadannan nasarorin za su taimaka wajen warware matsalolin da manoma ke fuskanta tare da bunkasa tattalin arzikin kasa wanda zai kai Nijeriya ga dogaro da kai a wajen samar da abinci ga ‘yan kasa.
Ya kuma bayyana cewa, a tsawon shekara 100 da kafa Cibiyar Binciken Harkokin Noma (IAR) na Samaru ta gudabar da bincike da dama a kan kayyakin noma daban-daban wadanda suka kai ga kara yabanyar da manoma ke samu da kuma bunkasa tattalin arzikinsu gaba daya.
A nashi jawabin, shugaban kwamitin samar da irin ‘TELA Maize’ a Nijeriya, Farfesa Rabiu Adamu, ya ce,an fara bincike don samar da irin a Nijeriya ne tun a shekarar 2019 an kuma yi haka ne saboda matsalolin da kwarin ‘Fall armyworm’ da ‘Stem-borers’ ke haifarwa a kan masara wanda hakan ke janyo asarar fiye kashi 80 na masarar da ake nomawa a fadin kasar nan.
Farfesa Rabiu Adamu wanda masani ne a bangaren kwari da yadda suke barnata shuka, ‘Entomology’, ya ce, samar da irin ‘TELA Maize’, zai taimaka wajen rage yadda manoma ke amfani da magunguna kashe kwari wanda hakan zai takaita yadda amfanin dasu ke cutar da muhalli da rayuwar al’umma. Ya ce, samar da ‘Tela Maize aiki ne na wata hadaka data hada da Gidauniyar Inganta Aikin Gona ta Afrika (AATF) a kasasshen Afrika 7 wanda suka hada da Kenya, Uganda, Tanzania, Ethiopia, Mozambikue, Nijeriya da kuma Afrika ta Kudu.
Manoman sun yi maraba tare da nuna jin dadinsu a kan samar da ‘Tela Maize’ wanda suka ce, tabbass zai bunkasa harkar noma a Nijeriya.

Tela Maize
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Bishiyar Dogon-yaro

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Bishiyar Dogon-yaro

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.