ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Sha’anin Noman Abarba Ke Taimakawa Kyautata Zaman Rayuwar Mazauna Wasu Kauyuka A Kasar Sin

by CGTN Hausa
1 year ago
Abarba

Kwanan baya, na ziyarci kauyen Yugonglou na gundumar Xuwen dake birnin Zhanjiang na lardin Guangdong, wurin da ya shahara da noman abarba a kasar Sin. Yayin da na shiga gonakin abarba marasa iyaka, na gano dalilin da ya sa ake yiwa gonakin take da “Tekun abarba”. Mazauna kauyen dake kokarin girbin abarba sun gaya min cewa, dukkanin mazauna kauyen suna ayyuka masu alaka da abarba, don haka ana iya cewa, a kashin kan ta abarba na kawo arziki ga wannan kauye.

Alkaluman da aka samar sun shaida cewa, a shekarar 2023, fadin gonakin da aka shuka abarba a gundumar Xuwen ya kai fiye da hekta dubu 22, kuma yawan abarba da aka samar ya zarce ton dubu 788, yayin da kudin da aikin ya samar ya kai sama da dalar Amurka miliyan 751. Inda ya taimaka wajen samar da guraben aikin yi dubu 146. Ana jigilar abarba da aka girba daga gonaki zuwa kamfanonin sarrafa ta iri daban-daban, daga baya suna shiga kasuwannin cikin gida da na waje.

  • Kasar Sin Ta Soki Zargin Da Philippines Ta Yi Mata Na Gina Tsibiri A Kusa Da Sashen Tudun Ruwa Na Xianbin Jiao
  • Kenya: An Kammala Baje Kolin Harkokin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afrika

Amma, a shekarun baya can, mazauna gundumar Xuwen masu shuka abarba, suna takaicin rashin sayar da su, har sun rube a gonaki. Da ganin hakan, gundumar Xuwen ta gaggauta raya kanta bisa shirin gwamnatin lardin Guangdong na raya ingantattun birane da gundumomi da kauyuka, inda ba ma kawai ta kafa cibiyar samar da alkaluma dake ba da taimako ga manoma wajen zabar nau’o’in abarba da tabbatar da farashinta da sauran bangarori ba, har ma da gaggauta raya sha’anin yawon shakatawa dake da alaka da al’adun abarba.

ADVERTISEMENT

Ta haka, na shiga otel din da aka gyara bisa gidajen mazauna kauyen, inda na ga gonakin abarba marasa iyaka, tare da jin kamshin abarba. Ba shakka yadda ake raya sha’anin yawon shakatawa mai alaka da al’adun abarba za ta kara kudin shigar mazauna kauyen.

An ce, ko wadanne abarba uku da aka samar a nan kasar Sin, daya daga cikinsu asalin Xuwen ce. Na debi wani na dandana, ruwan abarba mai zaki ya fito nan da nan, kamshi na cike da baki na, abin da ya alamanta zaman rayuwa mai zaki ta jama’ar wannan kauye. (Mai zana da rubuta: MINA)

LABARAI MASU NASABA

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam
Daga Birnin Sin

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa
Daga Birnin Sin

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya
Daga Birnin Sin

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
Next Post
Amurka

Gwamnati Ta Dakatar Da Harajin Tsaron Intanet Kan Hada-hadar Kudade

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.