• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Sa-kai Suka Lakada Wa Alaramma Duka Har Lahira A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Al'ajabi
0
Yadda ‘Yan Sa-kai Suka Lakada Wa Alaramma Duka Har Lahira A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Alaramma Musa Mai Dori, sanannen malamin makarantar Isilamiya ne a Unguwar Dabai, wanda wasu ‘yan kungiyar sa-kai da ke Unguwar Kankare makwabciyar Unguwar Dabai a karamar Hukumar Gwale a Jihar Kano suka yi wa wannan mutum kisan gilla.

An samu rahoton cewa dukan da ‘yan kungiyar sa-kai suka yi wa Malam Musa Mai Dori a ofiahinsu ranar Lahadin da ta gabata bayan da wata ta zarge shi da laifin satar wani jariri sabuwar haihuwa, wanda yake kokarin cetowa daga cikin bola da aka jefar da shi ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

  • Sabuwar Shekarar Musulunci Ta 1444: Hikimar Jujjuya Lokaci Da Allah Yake Mana
  • Buhari Ya Mika Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Sufeton ‘Yansanda Tafa Balogun

Mai Dori ya kasasance yana da shekara 50 da haihuwa, sannan yana da matan guda biyu, Khadija da Sha’awa da ‘ya’ya 16.

Dan uwan mamacin, Muhammad Ashiru Salisu, wanda ya yi magana da manema labarai ya ce, abin da ya faru wani abu ne na rashin imani wanda kuma aka shirya shi, domin yaran da suka aikata wannan aika-aika sun san malamin kwarai da gaske.

Salisu ya ci gaba da cewa, alaramman yana da kyakkyawar mu’amala ga dukkan mutanen da ke hankin.

Labarai Masu Nasaba

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

Ya ce, “Da yamma muka samu labarin kisan gillar da wasu ‘yan kungiyar sa-kai na unguwar Kankare suka yi wa wannan mutum. “Lamarin ya faru da safe ne, mu kuma mun samu labarin da yamma, malam ya bar gidansa a wannan safiya, yayin wucewa ta hanyasa, sai ya ga wani jariri sabun haihuwa a cikin wani ramin bola, a kokarin ceton jaririn ne, wata mata da ke bayansa ta kama ihun cewa wai malamin yana son satar jaririn ne.

“Babu shakka al’ummar Unguwar Dabai sun yi alkawarin bin wannan lamarin har karshensa domin tabbatar da gaskiya ta yi halinta.

“Matasan yankin sun yi kokarin daukar fansa kan abin da ya faru, kasancewar malamin ya koyar da mafi yawancinsu, bayan haka kuma shi ne ke taimaka wa jama’a idan matsalar ta kunno kai. Suka ce suna zargin wannan wani shiryeyyen al’amari ne.”

A nasa bangaren, babban dan mamacin, Abdussalam Musa cewa ya yi, “An daki mahaifina har takai ga mutuwasa, rahoton likitoci ne ya nuna an yi ta dukansa a kirjinsa har sai da zuciyarsa ta fara kwararar da jini. Ba za mu bar wannan lamari ya mutu kamar yadda malam ya mutu ba. Za mu bi lamarin har zuwa karshensa,” in ji shi.

Rahotanni sun nuna cewa mutane bakwai da ake zargi da aikata wannan mummunar lamari an kama su suna hannun ‘yan sanda a Rijiyar Zaki da ke Jihar Kano.

Da aka tuntubi kwamandan kungiyar sa-kai na Jihar Kano, Shehu Rabi’u ya ce ofishinsa bai samu wannan labari ba, amma ya yi alkawarin bincikewa zai kuma sanar da manema labarai halin da ake ciki.

A nasa bangaren, kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce mutane shida da ake zargin aikata wannan laifi suna hannu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Sa-KaiAlarammaAlmajiraiIhuJaririkanoKisan gillaMataShekaZargi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasu Gwamnatocin Kasashe Sun Nanata Matsayinsu Na Tsaiwa Tsayin Daka Kan Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

Next Post

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Sanar Da Matakan Martani Ga Ziyarar Da Pelosi Ta Kai Taiwan

Related

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi
Al'ajabi

Manomi Ya Ceto Jaririya Da Aka Binne Da Ranta A Kebbi

1 month ago
Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 
Al'ajabi

Wani Matashi Ya Ƙone Kansa A Kano Saboda Yana Son Zuwa Aljanna 

1 month ago
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi
Al'ajabi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

2 months ago
An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

3 months ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

3 months ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

3 months ago
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Sanar Da Matakan Martani Ga Ziyarar Da Pelosi Ta Kai Taiwan

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Sanar Da Matakan Martani Ga Ziyarar Da Pelosi Ta Kai Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.