• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Sa-kai Suka Lakada Wa Alaramma Duka Har Lahira A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
Alaramma

Alaramma Musa Mai Dori, sanannen malamin makarantar Isilamiya ne a Unguwar Dabai, wanda wasu ‘yan kungiyar sa-kai da ke Unguwar Kankare makwabciyar Unguwar Dabai a karamar Hukumar Gwale a Jihar Kano suka yi wa wannan mutum kisan gilla.

An samu rahoton cewa dukan da ‘yan kungiyar sa-kai suka yi wa Malam Musa Mai Dori a ofiahinsu ranar Lahadin da ta gabata bayan da wata ta zarge shi da laifin satar wani jariri sabuwar haihuwa, wanda yake kokarin cetowa daga cikin bola da aka jefar da shi ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

  • Sabuwar Shekarar Musulunci Ta 1444: Hikimar Jujjuya Lokaci Da Allah Yake Mana
  • Buhari Ya Mika Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Sufeton ‘Yansanda Tafa Balogun

Mai Dori ya kasasance yana da shekara 50 da haihuwa, sannan yana da matan guda biyu, Khadija da Sha’awa da ‘ya’ya 16.

Dan uwan mamacin, Muhammad Ashiru Salisu, wanda ya yi magana da manema labarai ya ce, abin da ya faru wani abu ne na rashin imani wanda kuma aka shirya shi, domin yaran da suka aikata wannan aika-aika sun san malamin kwarai da gaske.

Salisu ya ci gaba da cewa, alaramman yana da kyakkyawar mu’amala ga dukkan mutanen da ke hankin.

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Ya ce, “Da yamma muka samu labarin kisan gillar da wasu ‘yan kungiyar sa-kai na unguwar Kankare suka yi wa wannan mutum. “Lamarin ya faru da safe ne, mu kuma mun samu labarin da yamma, malam ya bar gidansa a wannan safiya, yayin wucewa ta hanyasa, sai ya ga wani jariri sabun haihuwa a cikin wani ramin bola, a kokarin ceton jaririn ne, wata mata da ke bayansa ta kama ihun cewa wai malamin yana son satar jaririn ne.

“Babu shakka al’ummar Unguwar Dabai sun yi alkawarin bin wannan lamarin har karshensa domin tabbatar da gaskiya ta yi halinta.

“Matasan yankin sun yi kokarin daukar fansa kan abin da ya faru, kasancewar malamin ya koyar da mafi yawancinsu, bayan haka kuma shi ne ke taimaka wa jama’a idan matsalar ta kunno kai. Suka ce suna zargin wannan wani shiryeyyen al’amari ne.”

A nasa bangaren, babban dan mamacin, Abdussalam Musa cewa ya yi, “An daki mahaifina har takai ga mutuwasa, rahoton likitoci ne ya nuna an yi ta dukansa a kirjinsa har sai da zuciyarsa ta fara kwararar da jini. Ba za mu bar wannan lamari ya mutu kamar yadda malam ya mutu ba. Za mu bi lamarin har zuwa karshensa,” in ji shi.

Rahotanni sun nuna cewa mutane bakwai da ake zargi da aikata wannan mummunar lamari an kama su suna hannun ‘yan sanda a Rijiyar Zaki da ke Jihar Kano.

Da aka tuntubi kwamandan kungiyar sa-kai na Jihar Kano, Shehu Rabi’u ya ce ofishinsa bai samu wannan labari ba, amma ya yi alkawarin bincikewa zai kuma sanar da manema labarai halin da ake ciki.

A nasa bangaren, kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce mutane shida da ake zargin aikata wannan laifi suna hannu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Sanar Da Matakan Martani Ga Ziyarar Da Pelosi Ta Kai Taiwan

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Sanar Da Matakan Martani Ga Ziyarar Da Pelosi Ta Kai Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.