ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Sa-kai Suka Lakada Wa Alaramma Duka Har Lahira A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
4 years ago
Alaramma

Alaramma Musa Mai Dori, sanannen malamin makarantar Isilamiya ne a Unguwar Dabai, wanda wasu ‘yan kungiyar sa-kai da ke Unguwar Kankare makwabciyar Unguwar Dabai a karamar Hukumar Gwale a Jihar Kano suka yi wa wannan mutum kisan gilla.

An samu rahoton cewa dukan da ‘yan kungiyar sa-kai suka yi wa Malam Musa Mai Dori a ofiahinsu ranar Lahadin da ta gabata bayan da wata ta zarge shi da laifin satar wani jariri sabuwar haihuwa, wanda yake kokarin cetowa daga cikin bola da aka jefar da shi ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

  • Sabuwar Shekarar Musulunci Ta 1444: Hikimar Jujjuya Lokaci Da Allah Yake Mana
  • Buhari Ya Mika Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Sufeton ‘Yansanda Tafa Balogun

Mai Dori ya kasasance yana da shekara 50 da haihuwa, sannan yana da matan guda biyu, Khadija da Sha’awa da ‘ya’ya 16.

ADVERTISEMENT

Dan uwan mamacin, Muhammad Ashiru Salisu, wanda ya yi magana da manema labarai ya ce, abin da ya faru wani abu ne na rashin imani wanda kuma aka shirya shi, domin yaran da suka aikata wannan aika-aika sun san malamin kwarai da gaske.

Salisu ya ci gaba da cewa, alaramman yana da kyakkyawar mu’amala ga dukkan mutanen da ke hankin.

LABARAI MASU NASABA

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

Ya ce, “Da yamma muka samu labarin kisan gillar da wasu ‘yan kungiyar sa-kai na unguwar Kankare suka yi wa wannan mutum. “Lamarin ya faru da safe ne, mu kuma mun samu labarin da yamma, malam ya bar gidansa a wannan safiya, yayin wucewa ta hanyasa, sai ya ga wani jariri sabun haihuwa a cikin wani ramin bola, a kokarin ceton jaririn ne, wata mata da ke bayansa ta kama ihun cewa wai malamin yana son satar jaririn ne.

“Babu shakka al’ummar Unguwar Dabai sun yi alkawarin bin wannan lamarin har karshensa domin tabbatar da gaskiya ta yi halinta.

“Matasan yankin sun yi kokarin daukar fansa kan abin da ya faru, kasancewar malamin ya koyar da mafi yawancinsu, bayan haka kuma shi ne ke taimaka wa jama’a idan matsalar ta kunno kai. Suka ce suna zargin wannan wani shiryeyyen al’amari ne.”

A nasa bangaren, babban dan mamacin, Abdussalam Musa cewa ya yi, “An daki mahaifina har takai ga mutuwasa, rahoton likitoci ne ya nuna an yi ta dukansa a kirjinsa har sai da zuciyarsa ta fara kwararar da jini. Ba za mu bar wannan lamari ya mutu kamar yadda malam ya mutu ba. Za mu bi lamarin har zuwa karshensa,” in ji shi.

Rahotanni sun nuna cewa mutane bakwai da ake zargi da aikata wannan mummunar lamari an kama su suna hannun ‘yan sanda a Rijiyar Zaki da ke Jihar Kano.

Da aka tuntubi kwamandan kungiyar sa-kai na Jihar Kano, Shehu Rabi’u ya ce ofishinsa bai samu wannan labari ba, amma ya yi alkawarin bincikewa zai kuma sanar da manema labarai halin da ake ciki.

A nasa bangaren, kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce mutane shida da ake zargin aikata wannan laifi suna hannu.

Alaramma
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

MASU ALAKA

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Al'ajabi

Ɓata-gari Sun Kashe Matar Aure Da ’Ya’yanta 3 A Kano

January 21, 2026
Next Post
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Sanar Da Matakan Martani Ga Ziyarar Da Pelosi Ta Kai Taiwan

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Sanar Da Matakan Martani Ga Ziyarar Da Pelosi Ta Kai Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.