• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Shiga Wani Gari Suka Ci Kaji Da Sakwara

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Yadda ‘Yan Ta’adda Suka Shiga Wani Gari Suka Ci Kaji Da Sakwara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan gudun hijira a Karamar Hukumar Shiroro da ke Jihar Neja sun koka kan yadda ‘yan ta’adda suka mayar da yankinsu sansaninsu na dindindin, inda suka shiga suka yayyanka musu kaji gami da daka sakwara da kuma kwashe kayan abincin da suka tanada a cikin shagunansu.

Da yake zantawa da manema labarai a Kuta kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, Ahmed Almustapha, wani dan gudun hijira daga Rumace-Madalla, ya koka da cewa yayin da suke fama da yunwa a sansaninsu, ‘yan ta’adda sun ci sun cika cikinsu abincin da suka tanada da dabbobinsu.

  • Yadda Gidan Buhari Ya Zama Fadar Ziyarar Jiga-jigan ‘Yan Siyasa
  • Falalar Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)

“Ba mu da jami’an tsaro a cikin al’ummarmu tun bayan janye sojoji daga Allawa. Tun daga wannan lokacin wadannan ‘yan ta’adda sun shafe kwanaki suna kashe mutane fiye da kowane lokaci. ‘Yan fashin sun mayar da yankinmu gidajenssu, su kwana a can suna cin abincin da muka bari a gida. Suna yanka mana kaji su yi miya da su, sannan su cinye mana doya, duk da haka har yanzu ba mai kalubalantar su.

“Tun bayan janyewar wadannan sojoji, mun yi asarar akalla mutu, 50; kuma da yawa an yi garkuwa da su. Makonni uku da suka gabata, an yi garkuwa da mutum 30 a Kauyukan Karaga, Kiriga da Agwaja; kuma har zuwa wannan lokacin, barayin ba su tuntubi kowa ba. Ba mu san inda suke ba ko kuma abin da suke yi da su,” in ji shi.

Rabi’u Iliyasu daga Garin Bassa ya ce duk ‘ya’yansa ba sa zuwa makaranta ne saboda ba shi da wani abin da zai sake daukar nauyin karatunsu.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Ya ce, “Duk ’yan uwana suna tare da ni a sansanin. Wasu daga cikin al’ummarmu suna Erena, yayin da wasu suka gudu zuwa sansanin Gwada. Ina tare da matata a sansanin Kuta. ’Yata tana karatau a Kwalejin Fasaha ta Tarayya da ke Kuta yayin da wasu kuma suna sauran makarantu. Na janye su ne saboda babu abin da zan daukar nauyin karatunsu.

“Ina da ‘ya’ya 17 da ke tsakanin shekaru 7 zuwa 13 da ke karkashin kulawata, ciki har da marayu da aka kashe iyayensu.

“A halin yanzu, ina wasu kananan ayyuka domin tsira da mutuncina. An yanka mahaifin daya daga cikin yaran da suke tare da ni kwanan nan. An yi garkuwa da mahaifiyar daya daga cikinsu shekaru uku da suka gabata bayan kashe mahaifin; kuma har yanzu ba mu ji komai game da ita ba. ‘Yan bindigar sun bukaci Naira miliyan 3 da babur a matsayin kudin fansa, mun biya su har ma da babur amma ba su sake ta ba. Daga baya mun samu labarin an kashe ta ne bayan an kai musu Naira miliyan uku da babur,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: NejaSakwara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilin Tashin Farashin Wake A Nijeriya

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke Kansila Da Hakimi Kan Zargin Satar Taransifoma A Gombe

Related

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

1 day ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

1 day ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

1 week ago
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

1 week ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

1 month ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

1 month ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Kansila Da Hakimi Kan Zargin Satar Taransifoma A Gombe

‘Yansanda Sun Cafke Kansila Da Hakimi Kan Zargin Satar Taransifoma A Gombe

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.