• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yansanda Suka Min Duka Kamar Dan Ta’adda – Shugaban NLC

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
NLC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kungiyar Kwadago na Kasa (NLC), Kwamared Joe Ajaero, ya labarto yadda ta kaya da shi a lokacin da ya tsinci kansa a hannun ‘yansanda da kuma ‘yan daba yayin da aka masa biji-biji sa’ilin da suka shirya zanga-zanga a Jihar Imo.

Ajaero, wanda ke bayanin abun da ya faru a ganawarsa da ‘yan jarida a Abuja, ya ce, jami’an ‘yansandan da ke karkashin Jihar Imo ne suka kama shi, suka masa dukan tsiya, suka nemi makantar da shi tare da jan sa a kasa kamar dan ta’adda.

  • Ribadu Ya Bukaci NLC Ta Janye Yajin Aiki, Ya Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Ajaero
  • Ba Ni Da Sha’awar Buga Wa Nijeriya Kwallo A Nan Gaba – Omorodion

Shugaban kwadago ya kuma karyata jita-jitan da ke yawo na cewa zanga-zangar da suka shirya yi a jihar ta siyasa ce. Ya ce zanga-zangar ta shafi yaki da rashin adalci da ake yi wa ma’aikata da kuma take musu hakki Jihar Imo.
Ya ce rashin jituwar da ake samu tsakanin kungiyar NLC da gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma na faruwa ne tun ma kafin ya zama shugaban NLC na kasa, don haka matsala ce wacce ta jima.

Ajaero ya ce NLC ba za taba ja da baya ba har sai lokacin da ma’aikata suka samu cikakken ‘yanci da walwala da kuma hakkokinsu.

Ya ce, “Jami’an ‘yansanda ne suka cafke ni suka duke ni da abubuwa daban-daban, inda suka tambayata mene ne ya sa nake kalubalantar gwamnan.

Labarai Masu Nasaba

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

“Su wadannan mutanen su ne kuma suka dauke ni zuwa shalkwatar ‘yansanda domin magana da ogansu, sun tsaya a waje kamar suna jiran wani kasurgumin dan ta’adda.

“A wajen, na rokesu kan cewa ina bukatar na sha wasu magunguna, amma suka yi ta tuhumata na tsawon awanni. Ina tunanin a wannan gabar ne suka kai ni zuwa ofishin kwamishinan ‘yansanda. Shi kuma ya umarcesu da su kaini asibitin ‘yansanda,” ya labarto.

A gefe daya kuma, babban sufeto ‘yansandan, Kayode Egbetokun, ya umarci a gudanar da bincike dangane da abubuwan da suka wakana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Joe AjaeroNlcTUC
ShareTweetSendShare
Previous Post

CGTN Ya Gabatar Da Shiri Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Next Post

Karancin Ruwan Sama A Nijar: Wasu Manoma Sun Koma Hakar Zinari

Related

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

2 hours ago
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
Labarai

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

3 hours ago
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna
Ra'ayi Riga

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

3 hours ago
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso
Labarai

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

4 hours ago
Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci
Labarai

Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

7 hours ago
NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3
Labarai

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3

8 hours ago
Next Post
Karancin Ruwan Sama A Nijar: Wasu Manoma Sun Koma Hakar Zinari

Karancin Ruwan Sama A Nijar: Wasu Manoma Sun Koma Hakar Zinari

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

An Fitar Da Kudaden Farfado Da Sassan Birnin Beijing Da Bala’in Ambaliyar Ruwa Ya Shafa

July 29, 2025
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

July 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin

July 29, 2025
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

July 29, 2025
Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

Mai Cin Moriyar Kai Da Mai Cin Moriyar Juna

July 29, 2025
Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

Kar Ka Zuga Ƴan Arewa Kan Tinubu — Nabena Ya Gargaɗi Kwankwaso

July 29, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci

July 29, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3

NiMet Ta Yi Hasashen Samun Mamakon Ruwan Sama A Sassan Nijeriya Cikin Kwana 3

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.