• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yansanda Suka Min Duka Kamar Dan Ta’adda – Shugaban NLC

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
NLC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kungiyar Kwadago na Kasa (NLC), Kwamared Joe Ajaero, ya labarto yadda ta kaya da shi a lokacin da ya tsinci kansa a hannun ‘yansanda da kuma ‘yan daba yayin da aka masa biji-biji sa’ilin da suka shirya zanga-zanga a Jihar Imo.

Ajaero, wanda ke bayanin abun da ya faru a ganawarsa da ‘yan jarida a Abuja, ya ce, jami’an ‘yansandan da ke karkashin Jihar Imo ne suka kama shi, suka masa dukan tsiya, suka nemi makantar da shi tare da jan sa a kasa kamar dan ta’adda.

  • Ribadu Ya Bukaci NLC Ta Janye Yajin Aiki, Ya Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Ajaero
  • Ba Ni Da Sha’awar Buga Wa Nijeriya Kwallo A Nan Gaba – Omorodion

Shugaban kwadago ya kuma karyata jita-jitan da ke yawo na cewa zanga-zangar da suka shirya yi a jihar ta siyasa ce. Ya ce zanga-zangar ta shafi yaki da rashin adalci da ake yi wa ma’aikata da kuma take musu hakki Jihar Imo.
Ya ce rashin jituwar da ake samu tsakanin kungiyar NLC da gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma na faruwa ne tun ma kafin ya zama shugaban NLC na kasa, don haka matsala ce wacce ta jima.

Ajaero ya ce NLC ba za taba ja da baya ba har sai lokacin da ma’aikata suka samu cikakken ‘yanci da walwala da kuma hakkokinsu.

Ya ce, “Jami’an ‘yansanda ne suka cafke ni suka duke ni da abubuwa daban-daban, inda suka tambayata mene ne ya sa nake kalubalantar gwamnan.

Labarai Masu Nasaba

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

“Su wadannan mutanen su ne kuma suka dauke ni zuwa shalkwatar ‘yansanda domin magana da ogansu, sun tsaya a waje kamar suna jiran wani kasurgumin dan ta’adda.

“A wajen, na rokesu kan cewa ina bukatar na sha wasu magunguna, amma suka yi ta tuhumata na tsawon awanni. Ina tunanin a wannan gabar ne suka kai ni zuwa ofishin kwamishinan ‘yansanda. Shi kuma ya umarcesu da su kaini asibitin ‘yansanda,” ya labarto.

A gefe daya kuma, babban sufeto ‘yansandan, Kayode Egbetokun, ya umarci a gudanar da bincike dangane da abubuwan da suka wakana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Joe AjaeroNlcTUC
ShareTweetSendShare
Previous Post

CGTN Ya Gabatar Da Shiri Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Next Post

Karancin Ruwan Sama A Nijar: Wasu Manoma Sun Koma Hakar Zinari

Related

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote
Labarai

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

33 minutes ago
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

2 hours ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

3 hours ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

11 hours ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

14 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

15 hours ago
Next Post
Karancin Ruwan Sama A Nijar: Wasu Manoma Sun Koma Hakar Zinari

Karancin Ruwan Sama A Nijar: Wasu Manoma Sun Koma Hakar Zinari

LABARAI MASU NASABA

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.