• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ‘Yansanda Suka Min Duka Kamar Dan Ta’adda – Shugaban NLC

by Khalid Idris Doya
2 years ago
NLC

Shugaban Kungiyar Kwadago na Kasa (NLC), Kwamared Joe Ajaero, ya labarto yadda ta kaya da shi a lokacin da ya tsinci kansa a hannun ‘yansanda da kuma ‘yan daba yayin da aka masa biji-biji sa’ilin da suka shirya zanga-zanga a Jihar Imo.

Ajaero, wanda ke bayanin abun da ya faru a ganawarsa da ‘yan jarida a Abuja, ya ce, jami’an ‘yansandan da ke karkashin Jihar Imo ne suka kama shi, suka masa dukan tsiya, suka nemi makantar da shi tare da jan sa a kasa kamar dan ta’adda.

  • Ribadu Ya Bukaci NLC Ta Janye Yajin Aiki, Ya Yi Allah Wadai Da Cin Zarafin Da Aka Yi Wa Ajaero
  • Ba Ni Da Sha’awar Buga Wa Nijeriya Kwallo A Nan Gaba – Omorodion

Shugaban kwadago ya kuma karyata jita-jitan da ke yawo na cewa zanga-zangar da suka shirya yi a jihar ta siyasa ce. Ya ce zanga-zangar ta shafi yaki da rashin adalci da ake yi wa ma’aikata da kuma take musu hakki Jihar Imo.
Ya ce rashin jituwar da ake samu tsakanin kungiyar NLC da gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma na faruwa ne tun ma kafin ya zama shugaban NLC na kasa, don haka matsala ce wacce ta jima.

Ajaero ya ce NLC ba za taba ja da baya ba har sai lokacin da ma’aikata suka samu cikakken ‘yanci da walwala da kuma hakkokinsu.

Ya ce, “Jami’an ‘yansanda ne suka cafke ni suka duke ni da abubuwa daban-daban, inda suka tambayata mene ne ya sa nake kalubalantar gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

“Su wadannan mutanen su ne kuma suka dauke ni zuwa shalkwatar ‘yansanda domin magana da ogansu, sun tsaya a waje kamar suna jiran wani kasurgumin dan ta’adda.

“A wajen, na rokesu kan cewa ina bukatar na sha wasu magunguna, amma suka yi ta tuhumata na tsawon awanni. Ina tunanin a wannan gabar ne suka kai ni zuwa ofishin kwamishinan ‘yansanda. Shi kuma ya umarcesu da su kaini asibitin ‘yansanda,” ya labarto.

A gefe daya kuma, babban sufeto ‘yansandan, Kayode Egbetokun, ya umarci a gudanar da bincike dangane da abubuwan da suka wakana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
Manyan Labarai

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Next Post
Karancin Ruwan Sama A Nijar: Wasu Manoma Sun Koma Hakar Zinari

Karancin Ruwan Sama A Nijar: Wasu Manoma Sun Koma Hakar Zinari

LABARAI MASU NASABA

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su

November 1, 2025
Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?

November 1, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.