ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Zaben Shugabannin Kungiyar Masu Maganin Gargajiya Ta Kasa Ya Gudana

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Gargajiya

Ranar Asabar da ta gabata ce, kungiyar masu sana’ar maganin gargajiya ta kasa ta gudanar da zaven shugabanninta na kasa waxanda za su tafiyar mata da harkokinta na shekaru huxu masu zuwa a xakin taro na otal din Kariya a karamar hukumar Karu na Jihar Nasarawa.

A shekaru 35 na kafa kungiyar, wannan shekarar ce aka zabi shugabannin kungiyar a kan tsarin zabe wanda kowa zai yi murna kan matakin da aka xauka na yin hakan, shekarun da suka gabata a kan yi nadi ne kawai.

  • Dabarar Siyasa Ta Balan-balan Ta Amurka
  • Karancin Kudi Ba Zai Shafi Zaben 2023 Ba —INEC 

Kafin a gudanar da zaven, sai aka bai wa ‘yan takarar mukaman mintuna, inda suka yi wa mabobinsu jawabi a kan abubuwan da za su yi wa ‘yan kungiyar da kuma kungiyar domin samun ci gaba da kowa zai ce sam barka.
Dan takarar muqamin mataimakin shugaban qungiya na Arewa ta tsakiya,

ADVERTISEMENT

Dakta Baba Audu Boka ya yi wani jawabi wanda ya burge mambobin da ke cikin xakin taron, inda ya ce idan aka zave shi a muqamin zai rika ilmintar da matasa abubuwa daban-daban dangane da maganin gargajiya.

An zabi mutane 23 waxanda za su jagoranci harkokin kungiyar na shekara hudu, da suka hada da Dakta Kabir Muhammed Naborgu a matsayin Shugaban kngiyar, Dakta Okpara Chigozie mataimakin a matsayin mataimakin Shugaban kungiyar, Honorabul (Dr) Abu Huraira Juwadu a matsayin Sakataren kungiya, Dakta Sani Bin Abdullahi a matsayin mai kula da jin dadin ‘yan kungiya, Dakta Goni Ali Hassan a matsayin mataimakin Shugaban kungiyar na Arewa maso gabas, Dakta Ishak Haruna a matsayin Sakataren tsare- tsare, Dakta Fatimatu Yakubu a matsayin Shugabar mata ta Arewa, Dakta Hashiru Halilu a matsayin mataimakin Shugaban kungiyar na Arewa maso yamma.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Sauran sun hada da Dakta Hadiza Ibrahim a matsayin Shugabar mata Arewa ta tsakiya, Dakta Jabbi Muhammed Bawa a matsayin Ma’aji na kungiyar, Dakta Nancy Chinyere a matsayin shugaban kungiyar ta Kudu maso gabas, Dakta Sa’adatu Isma’ila Haruna a matsayin Sakatariyar harkokin kudi, Dakta Nasiru Kaduna a matsayin mai tsawatarwa na kungiyar. Sauran sun hada da Honorabul (Dr) Abubkar Usman a matsayin mai binciken yadda aka kashe kudi, Dakta Baba Audu Boka a matsayin mataimakin shugaban kungiyar na Arewa ta tsakiya, Dakta Abubakar Tahir a matsayin Darektan ayyuka da horarwa, Dakta Abdullahi Idris Muhammed a matsayin Darekan bincike, Dakta Hassan Baba a matsayin mai tsawatarwa, Dakta Adamu Ningi a matsayin shugaban ‘ya’yan kungiya, Dakta Shafi’u Sardaunan Garu a matsayin jakadan kungiya, Dakta Sani Garba NCP, Dakta Ibrahim Abdul a matsayin Jami’in hulda da jama’a.

Gargajiya
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
De Gea Ya Buga Wasanni 400 A Gasar Firimiya

De Gea Ya Buga Wasanni 400 A Gasar Firimiya

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.