• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Zamfarawa Suka Karbi Tuban Kasurgumin Dan Bindiga Bello Turji

Tubansa Ba Alheri Ba Ne – Barista Bulama

by Hussein Yero
3 years ago
in Rahotonni
0
turji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon wannan makon ne Gwamnatin Jihar Zamfara ta tabbatar da cewa kasurgumin dan bindigar nan, Bello Turji, ya tuba daga barnar da suke yi, ya rungumi zaman lafiya kuma har ma ya zamo mata kwamandan yakar wadanda suka ki amincewa da sulhu kamar yadda Mataimakin Gwamnan Zamfara, Sanata Hassan Nasiha ya bayyana.

Mataimakin gwamnan ya ce Bello Turji, ya rungumi shirin zaman lafiya, ya kuma daina kai hare-hare a kananan hukumomin Birnin Magaji, Shinkafi da kuma Zurmi da ke fadin jihar.

  • Wani Makusancin Gwwamna Wike, Prince Nwiyor, Ya Fice Daga PDP Ya Koma APC

Ya bayyana haka ne a wani taro kan harkokin tsaro a Gusau babban birnin Jihar Zamfara, wanda kungiyar dalibai ta Jami’ar Madina ta shirya, inda ya ce matakin da Turji ya dauka na samar da zaman lafiya a kananan hukumomin guda uku wadanda a baya suke kan gaba wajen hare-haren ‘yan bindiga a Zamfara da ke arewa maso yammacin Nijeriya abin a yaba ne.

A cewar mataimakin gwamnan na Jihar Zamfara, a cikin makonni biyar da suka gabata ba a samu wata arangama tsakanin Fulani da Hausawa a kananan hukumomin Birnin Magaji, Shinkafi da Zurmi ba sakamakon tattaunawar sulhun da aka yi a tsakanin bangarorin biyu da ke fada da juna.

Ya bayyana cewa, Turji ya ba da umarnin a yi wa Gwamna Bello Muhammed albishir, domin a yanzu haka yana kaddamar da farmaki a kan ‘yan ta’addan da ake zargi a yankunan saboda tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali sun dawo jihar.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Sanata Nasiha ya kuma bayyana cewa kwamitin da Gwamna Bello Mohammed ya kafa a karkashinsa ya gudanar da taron zaman lafiya da sansanonin ‘yan bindiga guda 9 a gundumar Magami da Masarautar Dansadau ta kananan hukumomin Gusau da Maru ta jihar, domin dakatar da kai wa al’umma hare-haren da ba su ji ba ba su gani ba.

Ya ce Gwamna Matawalle ya bayar da umarnin a mayar da duk hanyoyin kiwo da filayen kiwo da ruwan da dabbobi suke amfani da sauran dukiyoyin Fulani da aka kwace a sakamakon rikicin da ya barke tsakanin su da Hausawa, kana ya ce a gaggauta mayar da su ga Fulani domin a samu zaman lafiya a kasa.

To ko yaya Zamfarawa suka karbi tuban Bello Turji ganin cewa akwai abubuwa marasa dadi da suka auku a tsakaninsa da al’ummomin gari?
Wani mazaunin garin Shinkafi, Malam Garba Gero ya nunar da cewa tuban Bello Turji abin lale marhabin ne domin wannan tsarin na sulhu shi ne zai taimaki yankinsu ya ceto su daga hadarin da suke ciki.

“’Yan’uwanmu na wajen Zamfara sun fid da rai daga gare mu tun da sun ba mu shawarwarin mutashi mun ki, kuma gashi sai kashe mu ake yi da sace mu, amma a yanzu Allah ya kawo karshen wahalar da muka sha a baya.
“Yanzu muna iya zuwa gonakinmu muna aiki ba tare da zullumi ba. Don haka muna murna da wannan sulhu na Turji da gwamnati ta amsa.”

Shi kuwa, Kabiru Moriki Direba, ya bayyana wa wakilinmu cewa, wannan sulhu alhairi ne.
“Domin yanzu haka mu direbobi ba mu tsoran hanya saboda ‘yan fashin daji, sai dai barayin gida masu amsar waya da kudi ba dai masu garkuwa da mutane ba. Yau wata biyu kenan mun samu kwaciyar hankali, fatar mu shi ne mu ga dorewarsa.”

Har ila yau, shi ma da yake bayyana ra’ayinsa, Hon. Abdullahi Muhammad Lakwaja Anka ya yaba wa Gwamna Matawalle bisa wannan namijin kokarin na maida ‘yan ta’adda mutanen kirki da ajiye makamansu tare da rungumar zaman lafiya.

“Muna kira ga Gwamna Matawalle da ya ci gaba a kan kokarinsa da yake yi na ganin su ma sauran ‘yan bindigan na yankin Anka, Gumi da Bukuyum sun aje makamansu. Tun da tsaurinsu ba su kai na Turji ba, amma gashi ta hannun Gwamna Matawalle an samu nasara a kan haka.
“Domin haka, muna yi wa kwamitin mataimakin gwamna a kan sulhu addu’a a kan samun nasara na dawamamen zaman lafiya a Jihar Zamfara gaba daya.”

Sai dai kuma, sauran ‘Yan Nijeriya masu lura da abubuwan da ke gudana na rashin tsaro a Zamfara, sun bayyana cewa bai kamata Bello Turji ya ci bulus kan abubuwan da ya aikata ba.
Mai sharhi kan ayyukan ‘yan ta’adda da harkokin yau da kullum, Barista Audu Bulama Bukarti ya ce sulhu da Turji ba zai haifar da da mai ido ba.

“Idan dai Turjin da muka sani ne wanda ya banka wa fasinjoji 23 ciki har da mace mai juna biyu wuta a Sakkwoto, yanzu kuma gwamnatin Zamfara ta ce ya tuba har yana taimaka mata wajen yakar ‘yan bindigan da suka ki yin sulhu, ba za mu yi mamaki ba idan gwamnatin ta saya masa makamai da motoci da sauran kayayyaki a matsayin yana taimaka mata.

“Har yanzu Turji bai yi nadama a kan kisan-kiyashin da ya yi ba. Domin a baya ya karya alkawarin da ya yi na sulhu. A yanzu haka yana zartar da hukunci a matsayin alkali na kisan wadansu ‘yan ta’adda, hakan ya ba shi lasisin ci gaba da kisan mutane kenan.

“Wannan sulhu zai iya kasancewa barazana, domin wasu gurbatattun ‘yan siyasa na iya amfani da shi a zabe mai zuwa wajen cimma burinsu. Lamarin zai kasance kamar alama ce ga sauran ‘yan ta’adda ta fuskar cewa abin da suke yi daidai ne kamar yadda Turji ya yi. Wannan ba zai haifar wa Jihar Zamfara da ma Nijeriya gaba daya da mai ido ba.” Kamar yadda ya bayyana a shafinsa na Facebook da aka tabbatar nasa ne.

Bukarti ya kara da cewa ya kamata Gwamnatin Zamfara ta fito fili ta yi wa jama’a cikakken bayani a kan wannan sabon yunkurin nata amma ba ta fara gutsura labari ta bar shi ba kamar yadda ita ma Rundunar ‘Yansandan jihar ta yi gum da bakinta kan lamarin.
Shi dai Aye Bello Turji asalin sunansa shi ne Muhammadu Bello, an haife shi a garin Fakai da ke Gundumar Kware a karamar hukumar Shinkafi ta Jihar Zamfara.

Shekarun Bello Turji ba su wuce 30 a duniya ba, ya taso ne a matsayin makiyayi karkashin mahaifinsa mai suna Kachalla.
Al’ummar yankin Fakai sun shaidi mahaifinsa a matsayin mutumin kirki, yana taka muhimmiyar rawa wajen sasanta kowacce irin fitina da ta taso a tsakanin Fulani da kuma Hausawa.

Mahaifin Turji ya bar yankin Shinkafi ne baki daya bayan da ya ga dansa Bello Turji ya dauki hanyar da ba ta dace ba, kuma ya yi iya bakin kokarinsa wajen ganin ya hana shi amma abin ya citura.
Bello Turji ya zama kasurgumin dan bindiga mai rike da makami tsawon shekara 7 da suka gabata. Ya bayyana daukar matakinsa ne da cewa sakamakon kisan da ‘yan kungiyar sa-kai suke yi wa Fulani tare da kona su da wuta, wanda a cewarsa ayyukansa na daukar fansa ne.

Bello Turji shi ne babban dan bindiga da ya addabi yankin Shinkafi a Jihar Zamfara da kananan hukumonin Isa da Sabon Birni da ke cikin Jihar Sakwato. Ya kashe mutanen da ko shi kansa bai san adadinsu ba a yankin karamar hukumar mulkin Shinkafi kawai. Akwai lokacin da a rana daya ya kashe sama da mutane 50 a yankin Kware, gundumar da ya fito.

A shekarar da ta gabata bayan da Gwamnatin Jihar Zamfara ta dauke layukan sadarwa na waya tare da kakaba dokar hana hawa babur da kuma takaita sayar da fetur a gidajen mai, ya mayar da hanyar Gusau zuwa Shinkafi kwata, inda a kullum sai an yi jana’izar mutane a Shinkafi wadanda yake kashewa a kan hanyar Kauran Namoda zuwa Shinkafi, haka kuma a kullum sai ya sace mutane matafiya ya kai su kauyensa na Fakai ana azabtar da su tare da neman kudin fansa.

Bello Turji ya farmaki garin Shinkafi safe da rana da kuma dare a lokuta mabanbanta har ma a masallaci ya kai hari ana tsaka da Sallar Magriba a garin Shinkafi, inda ya hallaka mutane 5 da raunata wasu da dama.
A watan Satumbar shekarar da ta gabata, ya rubuto doguwar takarda mai shafi uku zuwa ga Masarautar Shinkafi kargashin jagoranci Mai Martaba Muhammadu Makwashe Isa. Takardar na bayani ne a kan yana son a zauna lafiya kuma a ajiye makamai, sannan yana bukatar a isar da takardar zuwa ga Gwamnan Jihar Zamfara, Muhammad Bello Matawallen Maradun da kuma Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.
Bello Turji ya tsagaita bude wuta da satar mutane tun bayan da ya aike wa mahukunta wannan takardar ta neman sulhu.

Mahukunta a karamar hukumar Shinkafi sukan tuntubi Bello Turji idan aka samu matsalar tsaro a yankin, kuma yana iya bakin kokarinsa wajen ganin an shawo kan matsalar.

A watanni hudu da suka gabata, wani dan bindiga ya bulla a yankin Shinkafi wanda dan asalin garin Maniya ne da ke gundumar Badarawa a karamar hukumar Shinkafi, mai suna Dullum. Dan bindigar yakan tare mutane a hanyar Kauran Namoda zuwa Shinkafi yana kisa da sace wasu kuma yakan shiga garuruwa yana kisan mutane, musamman a garin Badarawa, Jangeru, Baice, Birnin Yero da sauransu.

Bello Turji ya gargadi Dullum a kan ya ajiye makamai, amma ya ki amincewa da gargadin da Bello Turji ya yi masa, inda yaransa suka yi fito-na-fito da Turji, ya samu nasarar aika shi lahira.

Zuwa yanzu dai yankin Shinkafi ana samun saukin hare-haren ‘yan bindiga, sai dai ba a rasawa a wasu yankuna, kuma idan Turji ya kama Bafulatani da sunan kai hari yana zartar masa da hukuncin kisa ne nan take, in ji wata majiya.

Al’ummar Fakai da kewaye sun tabbatar da cewa suna rayuwa ne irin ta bayi, domin Turji shi ne gwamnati a yankin, duk abin da ya tsara shi ake bi, kuma wanda ya saba masa yana zartas masa da hukunci mai tsanani.
Daga cikin dokokin da ya sanya har da hade masallatai. A baya akwai masallatan Juma’a biyu (Tsohon masallaci da kuma sabo mallakin kungiyar Izala) wanda daga bisani Turji ya yi umurnin haduwa a masallaci na daya domin gabatar da Sallar Juma’a. Zuwa yanzu dai Turji bai yi umurnin kungiyar Izala ta ci gaba da gabatar da Sallar Juma’a a masallacinta ba.

A yanzu haka a yankin mazauna garuruwan ne ke yi masa kowane aiki, kama daga aikin noma da kuma aikin ginin gida da masallaci da yake gudanarwa yanzu haka a Fakai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Darussa Ga Nijeriya Daga Zaben Kasar Kenya

Next Post

Kisan Gillar Sheikh Goni Aisami Gashuwa: Asalin Abin Da Ya Faru

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

2 weeks ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

2 weeks ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

3 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

3 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

4 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

4 weeks ago
Next Post
goni

Kisan Gillar Sheikh Goni Aisami Gashuwa: Asalin Abin Da Ya Faru

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 8-8-2025

GORON JUMA’A 8-8-2025

August 8, 2025
Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno

August 8, 2025
Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (1)

August 8, 2025
Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu

August 8, 2025
Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

Mamakon Ruwan Sama A Wasu Jihohi Na Barazana Ga Harkokin Yau Da Kullum

August 8, 2025
Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 

August 8, 2025
Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo

August 8, 2025
Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

August 7, 2025
Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

August 7, 2025
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.