• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaduwar Fasahar Juncao Ta Nuna Sahihancin Sin

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Yaduwar Fasahar Juncao Ta Nuna Sahihancin Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sinawa su kan ce, ba mutum kifi, bai kai koya masa dabarar su ba. Wannan ra’ayi na taimakon mutane ya nuna sosai, a kokarin kasar Sin na yayata fasahar Juncao a nahiyar Afirka.

 

A wajen wani bikin baje kolin fasahohin aikin gona da ya gudana a Kigali na kasar Rwanda a kwanan baya, wani mai masana’antu a kasar mai suna Emmanuel Ahimana ya ce, yadda ya samu damar koyon fasahar Juncao na kasar Sin ya sa shi farin ciki matuka. Ban da haka, duk a kwanan baya, Adhere Cavince, wani masharhanta na kasar Kenya, ya rubuta wani bayani da aka wallafa a jaridar Daily Nation ta kasar, wanda ya ce fasahar Juncao za ta taka rawar gani a kokarin kasar Kenya na kawar da talauci.

  • Jirgin Kasan Maglev Mai Saurin Gudu Ya Kammala Gwaji A Arewacin Kasar Sin
  • Jirgin Saman C919 Kirar Kasar Sin Ya Fara Zirga-zirga Kan Hanya Ta 5 

Juncao wani nau’in ciyawa ce da ake iya yin amfani da ita wajen noman laimar kwado, sa’an nan fasahar Juncao ta kunshi fannoni guda 2:

 

Labarai Masu Nasaba

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Na farko, noman ciyawar Juncao. Wannan ciyawa tana girma cikin matukar sauri, inda ake iya samun ciyayin ton 180 kan gonar kadada daya a duk shekara. Da wadannan ciyayi za a iya kiwon shanu 20. Ban da haka ciyayin na da daraja sosai a fannin kare halittu, ganin yadda nomansu ke iya kyautata yanayin kasa, da magance kwararar hamada.

 

Sa’an nan fanni na biyu game da fasahar Juncao shi ne, amfani da ciyayin Juncao wajen hada ledar noman laimar kwado, daga baya a dinga noman laimar kwado a kanta. Idan an kwatanta da fasahar gargajiya ta noman laimar kwado kan ice, wannan sabuwar fasaha ta fi samar da laimar kwado, gami da tabbatar da ingancinsu, da kare muhalli.

 

Wannan fasahar da kasar Sin ta samu a lokacin da take kokarin zamanintar da aikin gona, da rage talauci da raya kauyuka, tana taka rawar gani yanzu a kasashen Afirka, a fannonin samar da abinci, da rage talauci. Misali, wani matashi dan kasar Rwanda mai suna Mushimiyiman Leonidas ya samu damar koyon fasahar Juncao a kasar Sin a shekarar 2013. Bayan da ya kammala horo, ya koma Kigali, inda ya bude wata masana’anta. Zuwa yanzu masana’antarsa tana iya samar da ledar noman laimar kwado dubu 30 a duk wata, gami da laimar kwado kilo 600 a kowane mako. Yanzu a kasar Rwanda akwai iyalai fiye da 4000 da suke noman laimar kwado, sha’anin da ya ba mutane fiye da dubu 30 ayyukan yi.

 

Don nagartacciyar fasahar Juncao ta amfani karin mutane, kasar Sin ta dade tana kokarin yayata ta a duniya. Zuwa farkon shekarar bana, kasar Sin ta shirya kwasa-kwasai har guda 270 na koyar da fasahar Juncao, wadanda suka shafi mutane fiye da dubu goma daga kasashe daban daban. Yanzu haka, ban da Rwanda, an yada fasahar zuwa Najeriya, da Afirka ta Kudu, da Kenya, da Tanzania, da sauran kasashen dake nahiyar Afirka da dama. A cewar Amson Sibanda, jami’in hukumar kula da tattalin arziki da zaman al’umma ta MDD (UNDESA), fasahar Juncao za ta iya taimakawa kokarin cimma burin samun ci gaba mai dorewa na shekarar 2030, gami da yunkurin daidaita matsalar karancin abinci, da ta gurbacewar muhalli, da kuma talauci.

 

Yaduwar fasahar Juncao ta nuna ra’ayin Sinawa na “koyar da dabararsu maimakon bayar da kyautar kifi”, gami da tunaninta na hadin gwiwa da kasashen Afirka, wato gaskiya, da sahihanci, da kauna, da kuma haifar da hakikanan ci gaba. Duk darajar wata fasaha, idan dai za ta sanya kasashen Afirka samun hakikanin ci gaba, da kyautatuwar rayuwar jama’a, to, kasar Sin za ta yayata ta ba tare da wani jinkiri ba. A ganin Sinawa, wannan shi ne ra’ayi mai dacewa na hulda da abokai. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fasahar Zamani Na Taka Rawar Gani Ga Ci Gaban Masana’antu Sin

Next Post

Tinubu Ya Ba da Umarnin Kame Duk Masu Ɗaga Tutar Rasha Yayin Zanga-Zanga

Related

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

57 minutes ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

2 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

3 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

4 hours ago
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan
Daga Birnin Sin

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

5 hours ago
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

6 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Ba da Umarnin Kame Duk Masu Ɗaga Tutar Rasha Yayin Zanga-Zanga

Tinubu Ya Ba da Umarnin Kame Duk Masu Ɗaga Tutar Rasha Yayin Zanga-Zanga

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.