• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaduwar Fasahar Juncao Ta Nuna Sahihancin Sin

by Sulaiman and CGTN Hausa
12 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Yaduwar Fasahar Juncao Ta Nuna Sahihancin Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sinawa su kan ce, ba mutum kifi, bai kai koya masa dabarar su ba. Wannan ra’ayi na taimakon mutane ya nuna sosai, a kokarin kasar Sin na yayata fasahar Juncao a nahiyar Afirka.

 

A wajen wani bikin baje kolin fasahohin aikin gona da ya gudana a Kigali na kasar Rwanda a kwanan baya, wani mai masana’antu a kasar mai suna Emmanuel Ahimana ya ce, yadda ya samu damar koyon fasahar Juncao na kasar Sin ya sa shi farin ciki matuka. Ban da haka, duk a kwanan baya, Adhere Cavince, wani masharhanta na kasar Kenya, ya rubuta wani bayani da aka wallafa a jaridar Daily Nation ta kasar, wanda ya ce fasahar Juncao za ta taka rawar gani a kokarin kasar Kenya na kawar da talauci.

  • Jirgin Kasan Maglev Mai Saurin Gudu Ya Kammala Gwaji A Arewacin Kasar Sin
  • Jirgin Saman C919 Kirar Kasar Sin Ya Fara Zirga-zirga Kan Hanya Ta 5 

Juncao wani nau’in ciyawa ce da ake iya yin amfani da ita wajen noman laimar kwado, sa’an nan fasahar Juncao ta kunshi fannoni guda 2:

 

Labarai Masu Nasaba

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

Na farko, noman ciyawar Juncao. Wannan ciyawa tana girma cikin matukar sauri, inda ake iya samun ciyayin ton 180 kan gonar kadada daya a duk shekara. Da wadannan ciyayi za a iya kiwon shanu 20. Ban da haka ciyayin na da daraja sosai a fannin kare halittu, ganin yadda nomansu ke iya kyautata yanayin kasa, da magance kwararar hamada.

 

Sa’an nan fanni na biyu game da fasahar Juncao shi ne, amfani da ciyayin Juncao wajen hada ledar noman laimar kwado, daga baya a dinga noman laimar kwado a kanta. Idan an kwatanta da fasahar gargajiya ta noman laimar kwado kan ice, wannan sabuwar fasaha ta fi samar da laimar kwado, gami da tabbatar da ingancinsu, da kare muhalli.

 

Wannan fasahar da kasar Sin ta samu a lokacin da take kokarin zamanintar da aikin gona, da rage talauci da raya kauyuka, tana taka rawar gani yanzu a kasashen Afirka, a fannonin samar da abinci, da rage talauci. Misali, wani matashi dan kasar Rwanda mai suna Mushimiyiman Leonidas ya samu damar koyon fasahar Juncao a kasar Sin a shekarar 2013. Bayan da ya kammala horo, ya koma Kigali, inda ya bude wata masana’anta. Zuwa yanzu masana’antarsa tana iya samar da ledar noman laimar kwado dubu 30 a duk wata, gami da laimar kwado kilo 600 a kowane mako. Yanzu a kasar Rwanda akwai iyalai fiye da 4000 da suke noman laimar kwado, sha’anin da ya ba mutane fiye da dubu 30 ayyukan yi.

 

Don nagartacciyar fasahar Juncao ta amfani karin mutane, kasar Sin ta dade tana kokarin yayata ta a duniya. Zuwa farkon shekarar bana, kasar Sin ta shirya kwasa-kwasai har guda 270 na koyar da fasahar Juncao, wadanda suka shafi mutane fiye da dubu goma daga kasashe daban daban. Yanzu haka, ban da Rwanda, an yada fasahar zuwa Najeriya, da Afirka ta Kudu, da Kenya, da Tanzania, da sauran kasashen dake nahiyar Afirka da dama. A cewar Amson Sibanda, jami’in hukumar kula da tattalin arziki da zaman al’umma ta MDD (UNDESA), fasahar Juncao za ta iya taimakawa kokarin cimma burin samun ci gaba mai dorewa na shekarar 2030, gami da yunkurin daidaita matsalar karancin abinci, da ta gurbacewar muhalli, da kuma talauci.

 

Yaduwar fasahar Juncao ta nuna ra’ayin Sinawa na “koyar da dabararsu maimakon bayar da kyautar kifi”, gami da tunaninta na hadin gwiwa da kasashen Afirka, wato gaskiya, da sahihanci, da kauna, da kuma haifar da hakikanan ci gaba. Duk darajar wata fasaha, idan dai za ta sanya kasashen Afirka samun hakikanin ci gaba, da kyautatuwar rayuwar jama’a, to, kasar Sin za ta yayata ta ba tare da wani jinkiri ba. A ganin Sinawa, wannan shi ne ra’ayi mai dacewa na hulda da abokai. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fasahar Zamani Na Taka Rawar Gani Ga Ci Gaban Masana’antu Sin

Next Post

Tinubu Ya Ba da Umarnin Kame Duk Masu Ɗaga Tutar Rasha Yayin Zanga-Zanga

Related

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu
Daga Birnin Sin

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

14 hours ago
Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana
Daga Birnin Sin

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

15 hours ago
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing
Daga Birnin Sin

Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

16 hours ago
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika
Daga Birnin Sin

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

17 hours ago
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka
Daga Birnin Sin

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

20 hours ago
Sin Na Ci Gaba Da Kyautata Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Hidimomin Dijital Da Na Kirkirarriyar Basira
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Kyautata Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Hidimomin Dijital Da Na Kirkirarriyar Basira

21 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Ba da Umarnin Kame Duk Masu Ɗaga Tutar Rasha Yayin Zanga-Zanga

Tinubu Ya Ba da Umarnin Kame Duk Masu Ɗaga Tutar Rasha Yayin Zanga-Zanga

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 01-07-2025

August 1, 2025
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

August 1, 2025
Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

August 1, 2025
Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa

August 1, 2025
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

August 1, 2025
Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

August 1, 2025
Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni

Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni

August 1, 2025
Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul

Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul

August 1, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

July 31, 2025
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.