ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaduwar Fasahar Juncao Ta Nuna Sahihancin Sin

by Sulaiman and CGTN Hausa
2 years ago
Juncao

Sinawa su kan ce, ba mutum kifi, bai kai koya masa dabarar su ba. Wannan ra’ayi na taimakon mutane ya nuna sosai, a kokarin kasar Sin na yayata fasahar Juncao a nahiyar Afirka.

 

A wajen wani bikin baje kolin fasahohin aikin gona da ya gudana a Kigali na kasar Rwanda a kwanan baya, wani mai masana’antu a kasar mai suna Emmanuel Ahimana ya ce, yadda ya samu damar koyon fasahar Juncao na kasar Sin ya sa shi farin ciki matuka. Ban da haka, duk a kwanan baya, Adhere Cavince, wani masharhanta na kasar Kenya, ya rubuta wani bayani da aka wallafa a jaridar Daily Nation ta kasar, wanda ya ce fasahar Juncao za ta taka rawar gani a kokarin kasar Kenya na kawar da talauci.

ADVERTISEMENT
  • Jirgin Kasan Maglev Mai Saurin Gudu Ya Kammala Gwaji A Arewacin Kasar Sin
  • Jirgin Saman C919 Kirar Kasar Sin Ya Fara Zirga-zirga Kan Hanya Ta 5 

Juncao wani nau’in ciyawa ce da ake iya yin amfani da ita wajen noman laimar kwado, sa’an nan fasahar Juncao ta kunshi fannoni guda 2:

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Na farko, noman ciyawar Juncao. Wannan ciyawa tana girma cikin matukar sauri, inda ake iya samun ciyayin ton 180 kan gonar kadada daya a duk shekara. Da wadannan ciyayi za a iya kiwon shanu 20. Ban da haka ciyayin na da daraja sosai a fannin kare halittu, ganin yadda nomansu ke iya kyautata yanayin kasa, da magance kwararar hamada.

 

Sa’an nan fanni na biyu game da fasahar Juncao shi ne, amfani da ciyayin Juncao wajen hada ledar noman laimar kwado, daga baya a dinga noman laimar kwado a kanta. Idan an kwatanta da fasahar gargajiya ta noman laimar kwado kan ice, wannan sabuwar fasaha ta fi samar da laimar kwado, gami da tabbatar da ingancinsu, da kare muhalli.

 

Wannan fasahar da kasar Sin ta samu a lokacin da take kokarin zamanintar da aikin gona, da rage talauci da raya kauyuka, tana taka rawar gani yanzu a kasashen Afirka, a fannonin samar da abinci, da rage talauci. Misali, wani matashi dan kasar Rwanda mai suna Mushimiyiman Leonidas ya samu damar koyon fasahar Juncao a kasar Sin a shekarar 2013. Bayan da ya kammala horo, ya koma Kigali, inda ya bude wata masana’anta. Zuwa yanzu masana’antarsa tana iya samar da ledar noman laimar kwado dubu 30 a duk wata, gami da laimar kwado kilo 600 a kowane mako. Yanzu a kasar Rwanda akwai iyalai fiye da 4000 da suke noman laimar kwado, sha’anin da ya ba mutane fiye da dubu 30 ayyukan yi.

 

Don nagartacciyar fasahar Juncao ta amfani karin mutane, kasar Sin ta dade tana kokarin yayata ta a duniya. Zuwa farkon shekarar bana, kasar Sin ta shirya kwasa-kwasai har guda 270 na koyar da fasahar Juncao, wadanda suka shafi mutane fiye da dubu goma daga kasashe daban daban. Yanzu haka, ban da Rwanda, an yada fasahar zuwa Najeriya, da Afirka ta Kudu, da Kenya, da Tanzania, da sauran kasashen dake nahiyar Afirka da dama. A cewar Amson Sibanda, jami’in hukumar kula da tattalin arziki da zaman al’umma ta MDD (UNDESA), fasahar Juncao za ta iya taimakawa kokarin cimma burin samun ci gaba mai dorewa na shekarar 2030, gami da yunkurin daidaita matsalar karancin abinci, da ta gurbacewar muhalli, da kuma talauci.

 

Yaduwar fasahar Juncao ta nuna ra’ayin Sinawa na “koyar da dabararsu maimakon bayar da kyautar kifi”, gami da tunaninta na hadin gwiwa da kasashen Afirka, wato gaskiya, da sahihanci, da kauna, da kuma haifar da hakikanan ci gaba. Duk darajar wata fasaha, idan dai za ta sanya kasashen Afirka samun hakikanin ci gaba, da kyautatuwar rayuwar jama’a, to, kasar Sin za ta yayata ta ba tare da wani jinkiri ba. A ganin Sinawa, wannan shi ne ra’ayi mai dacewa na hulda da abokai. (Bello Wang)

Juncao
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • Sulaiman
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Juncao
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Next Post
Tinubu Ya Ba da Umarnin Kame Duk Masu Ɗaga Tutar Rasha Yayin Zanga-Zanga

Tinubu Ya Ba da Umarnin Kame Duk Masu Ɗaga Tutar Rasha Yayin Zanga-Zanga

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.