• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aiki: Gwamnatin Legas Za Ta Gana Da Direbobin Motoci Ranar Laraba 

by Sadiq
3 years ago
in Labarai
0
Yajin Aiki: Gwamnatin Legas Za Ta Gana Da Direbobin Motoci Ranar Laraba 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Legas ta ce an shirya wata ganawa da kungiyar jin dadin direbobi ta kasa JDWAN a kan yajin aikin da direbobi ke ci gaba da yi a ranar Laraba. 

Direbobin dai sun fara yajin aikin na kwanaki bakwai ne a ranar Litinin, bisa zarginsu da karbar kudaden da ake zargin hukumomin kula da wuraren shakatawa da gareji a jihar.

  • Xi Ya Jaddada Sake Farfado Da Yankunan Karkara Yayin Da Ya Ziyarci Shaanxi Da Henan
  • Dubun Wanda Ya Kashe Mahaifinsa Ta Cika A Legas

Wannan lamari ya sa matafiya da dama a jihar shiga damuwa a ranar Litinin, yayin da aka samu karin farashin kaya daga wajen masu ababen hawa.

A cikin wata sanarwa da gwamnatin Legas ta fitar, ta ce an gudanar da wani taro da kungiyar a ranar 28 ga watan Oktoba, inda aka sake yin wani taron a ranar Laraba.

A cewar sanarwar, mai ba gwamnan jihar shawara na musamman kan harkokin sufuri, Sola Giwa, ya kara da cewa gwamnatin Legas na duba bukatun direbobin “da nufin samar da mafita ta din-din-din kan batutuwan da kungiyar ta gabatar.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

“Ya bayyana cewa a ci gaba da sanarwar da JDWAN ta bayar na shiga yajin aikin kwanaki bakwai daga ranar 31 ga watan Oktoba, 2022, gwamnatin jihar ta hannun ma’aikatar sufuri ta gayyaci shugabanninta zuwa wani taro a ranar Juma’a 28 ga Oktoba, 2022, duk da rashin alakarta da wata kungiyar sufuri, irin su NURTW da RTEAN, da jihar ta sani,” in ji sanarwar.

“A cewarsa, yawancin ’yan kungiyar da suka halarci taron sun fito ne daga bangaren Badagry kuma an yanke shawarar dage taron har zuwa ranar Laraba 2 ga watan Nuwamba, 2022 don an hada da wakilan sauran kungiyoyin da aka amince da su tare da kungiyar duba da warware lamarin cikin ruwan sanyi.“

Yayin da ya ke bayyana sakamakon taron karo na biyu da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba ga jama’a, Giwa ya bukaci ‘yan kungiyar ta JDWAN da su ci gaba da gudanar da ayyukansu na yau da kullum ba tare da fargabar zagi da ko tsangwama ba domin an umarci hukumomin tsaro da su tabbatar da doka da oda.

Mashawarcin na musamman ya kuma gargadi wadanda ke cin gajiyar yajin aikin m “da su daina yin hakan ko kuma su fuskanci fushin hukuma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BadagryDirebobin MotociFasinjojiLegasYajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutuwar Dan Davido: PDP Ta Dakatar Da Tarukan Siyasa A Jihar Osun

Next Post

Kadarorina Na Sayar Na Dauki Nauyin Karatun Dalibai –Kwankwaso

Related

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

4 hours ago
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi
Labarai

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

5 hours ago
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo
Labarai

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

5 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

6 hours ago
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 
Labarai

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

7 hours ago
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372
Labarai

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

8 hours ago
Next Post
Kadarorina Na Sayar Na Dauki Nauyin Karatun Dalibai –Kwankwaso

Kadarorina Na Sayar Na Dauki Nauyin Karatun Dalibai –Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.