ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aiki: Gwamnatin Legas Za Ta Gana Da Direbobin Motoci Ranar Laraba 

by Sadiq
4 years ago
Legas

Gwamnatin Jihar Legas ta ce an shirya wata ganawa da kungiyar jin dadin direbobi ta kasa JDWAN a kan yajin aikin da direbobi ke ci gaba da yi a ranar Laraba. 

Direbobin dai sun fara yajin aikin na kwanaki bakwai ne a ranar Litinin, bisa zarginsu da karbar kudaden da ake zargin hukumomin kula da wuraren shakatawa da gareji a jihar.

  • Xi Ya Jaddada Sake Farfado Da Yankunan Karkara Yayin Da Ya Ziyarci Shaanxi Da Henan
  • Dubun Wanda Ya Kashe Mahaifinsa Ta Cika A Legas

Wannan lamari ya sa matafiya da dama a jihar shiga damuwa a ranar Litinin, yayin da aka samu karin farashin kaya daga wajen masu ababen hawa.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da gwamnatin Legas ta fitar, ta ce an gudanar da wani taro da kungiyar a ranar 28 ga watan Oktoba, inda aka sake yin wani taron a ranar Laraba.

A cewar sanarwar, mai ba gwamnan jihar shawara na musamman kan harkokin sufuri, Sola Giwa, ya kara da cewa gwamnatin Legas na duba bukatun direbobin “da nufin samar da mafita ta din-din-din kan batutuwan da kungiyar ta gabatar.

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

“Ya bayyana cewa a ci gaba da sanarwar da JDWAN ta bayar na shiga yajin aikin kwanaki bakwai daga ranar 31 ga watan Oktoba, 2022, gwamnatin jihar ta hannun ma’aikatar sufuri ta gayyaci shugabanninta zuwa wani taro a ranar Juma’a 28 ga Oktoba, 2022, duk da rashin alakarta da wata kungiyar sufuri, irin su NURTW da RTEAN, da jihar ta sani,” in ji sanarwar.

“A cewarsa, yawancin ’yan kungiyar da suka halarci taron sun fito ne daga bangaren Badagry kuma an yanke shawarar dage taron har zuwa ranar Laraba 2 ga watan Nuwamba, 2022 don an hada da wakilan sauran kungiyoyin da aka amince da su tare da kungiyar duba da warware lamarin cikin ruwan sanyi.“

Yayin da ya ke bayyana sakamakon taron karo na biyu da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba ga jama’a, Giwa ya bukaci ‘yan kungiyar ta JDWAN da su ci gaba da gudanar da ayyukansu na yau da kullum ba tare da fargabar zagi da ko tsangwama ba domin an umarci hukumomin tsaro da su tabbatar da doka da oda.

Mashawarcin na musamman ya kuma gargadi wadanda ke cin gajiyar yajin aikin m “da su daina yin hakan ko kuma su fuskanci fushin hukuma.

MASU ALAKA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53
Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Next Post
Kadarorina Na Sayar Na Dauki Nauyin Karatun Dalibai –Kwankwaso

Kadarorina Na Sayar Na Dauki Nauyin Karatun Dalibai –Kwankwaso

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Safarar Kuɗi Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.