• English
  • Business News
Thursday, August 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aiki: NAHCON Ta Gargadi NLC Kan Janyo Cikas Ga Jigilar Maniyyata

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
NAHCON
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da jin dadin alhazai ta kasa (NAHCON), ta gargadi kungiyar kwadago (NLC) dangane janyo cikas ga ci gaba da aiki jigilar maniyyata daga nan gida Nijeriya zuwa kasar Saudiyya Arabiyya sakamakon yajin aiki. Mataimakiyar daraktan sashin yada labarai na NAHCON, Misis Fatima Usara, ita ce ta yi gargadin a wata sanarwar da ta fitar a Abuja.

Usara ta nemi NLC da ta gane hatsarin da ke cikin janyo cikas da tarnaki ga jigilar maniyyatan aikin hajjin bana. Ta nuna cewa kamata ya yi NLC ta taimaki duk wani motsi na samun nasarar kwasan maniyyata ba wai janyo cikas ba.

  • Alhazan Abuja Da Kogi Sun Yaba Wa Ƙoƙarin NAHCON A Madina
  • NAHCON Ta Karyata Rahoton Bayar Da Abinci Mara Inganci Ga Alhazai A Makkah

“Bayanai sun riski NAHCON da ke nuni da cewa akwai shirye-shiryen da wasu bangaren NLC ke yi na kokarin kawo cikas na jigilar maniyyata aikin hajji da ake kan gudanarwa.
“Wannan na zuwa ne duk da kyakkyawar fahimtar juna da aka cimma na cewa babu abun da zai shafi jiragen da ke jigilar maniyyata sakamakon shiga yajin aiki.

“Hukamarmu ta jinjina wa damuwar da NLC ta nuna kan tabbatar da walwala da jin dadin mambobinta, amma NAHCON na son a mutunta damar zuwa aikin hajji ga Musulman da suka samu dama.
“Hukumar ta shawarci NLC da ta yi taka-tsan-tsan ka da ta yi katsalandan wajen janyo cikas domin mutunta addinin Musulunci.

“Janyo duk wata cikas ko jinkiri ga aikin jigilar alhazai ka iya janyo a tauye wa Musulmai masu niyyar zuwa aikin hajji hakkinsu da ‘yancinsu na yin ibada lura da dan kankanin lokacin da aka ware domin rufe filayen jiragen Jeddah da Madinah ga maniyyata,” sanarwar ta shaida.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

A kalla maniyyata dubu 65,500 daga Nijeriya ne ake sa ran za su gudanar da aikin hajji a can kasa mai tsarki a shekarar 2024.

NAHCON ta yi jigilar maniyyata sama da 38,805 zuwa Saudiyya a jirage 92 daban-daban.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AlhajiAlhazaiHajjiHukumar NAHCONMadinaMeccaNAHCON
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Gombe Ya Gwangwaje Shugabannin Kananan Hukumomi Da Motoci

Next Post

Ƴan Bindiga Sun Yi Taɓargaza, Sun Kashe Ƴansanda 7 Da Wasu A Katsina

Related

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16
Labarai

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

55 minutes ago
Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina
Manyan Labarai

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

2 hours ago
Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara
Labarai

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

10 hours ago
APC
Labarai

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

12 hours ago
Tinubu
Labarai

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

13 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

15 hours ago
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Yi Taɓargaza, Sun Kashe Ƴansanda 7 Da Wasu A Katsina

Ƴan Bindiga Sun Yi Taɓargaza, Sun Kashe Ƴansanda 7 Da Wasu A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16

August 14, 2025
Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

Yadda Ƙananan Hukumomi Ke Yin Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina

August 14, 2025
Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwamnan Zamfara

August 13, 2025
Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

Gyaruwar Alakar Kasuwancin Sin Da Amurka Ta Zarce Bukatun Kasashen Biyu

August 13, 2025
APC

2027: Jagororin APC Na Kudu-maso-Yamma Sun Amince Da Tinubu Ya Sake Tsayawa Takara

August 13, 2025
Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

Sin Ta Dauki Matakan Mayar Da Martani Kan Bankuna Biyu Na EU

August 13, 2025
Tinubu

Rangwame: Tinubu Ya Bada Umarnin Sake Bitar Tsarin Yadda Ake Karɓar Haraji 

August 13, 2025
Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

Sashen Tattalin Arzikin Teku Na Sin Ya Bunkasa A Rabin Farko Na Bana

August 13, 2025
Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

Farfado Da Karkarar Sin: Canjin Gaisuwa Daga “Shin Ka Ci Abinci?” Zuwa “Yaya Rayuwarka A Gari?”

August 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.