• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ASUU: NLC, ASUU da Sauran Kungiyoyi Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Lumana A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
in Kananan Labarai
0
Yajin Aikin ASUU: NLC, ASUU da Sauran Kungiyoyi Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Lumana A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Kwadago Ta Kasa reshen Jihar Kebbi (NLC), tare da Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) da sauran kungiyoyi sun gudanar da zanga-zangar lumana a manyan titunan birnin Kebbi, a jihar Kebbi kan goyon bayan yajin aikin da ASUU ke yi.

Karkashin jagorancin shugaban kungiyar NLC reshen jihar Kebbi, Kwamared Umar Halidu Alhasaan, masu zanga-zangar dauke da rubuce-rubuce daban-daban, kamar “kawo karshen yajin aikin ASUU yanzu, rufe jami’o’i yana da illa ga tattalin arziki, siyasa, likitanci, al’umma da shari’a.

  • Zaben Fidda-Gwanin PDP: Kotu Ta Fara Sauraren Karar Dan Majalisar Argungu/Augie a Kebbi
  • NNPP Ga Buhari: Ka Sanya Dokar Ta Baci A Jihohin Arewa 5

Haka kuma ya zama damuwa ga zaman ‘ya’yanmu a gida wanda ba karamin matsala zai haifar ga yaranmu da mu kan mu iyaye.

Bisa ga hakan muna kira ga gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu, ya sa baki domin kawo karshen yajin aikin malaman jami’o’in kasa nan .

Da yake jawabi shugaban NLC a jihar Kebbi, Kwamared Umar Halidu Alhassan ya bayyana cewa “Shugabanni kwadagon sun fito kan tituna domin gudanar da zanga-zangar domin daliban da abin ya fi shafa su ne ‘ya’yan talakawa da ke makarantun gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

“ASUU ta shiga yajin aikin watanni biyar da suka gabata, kuma mafi yawan wadanda abin ya shafa ‘ya’yan talakawa ne, abin da muke yi a yau ba wai don kawo karshen yajin aikin ba ne, sai dai fafutukar ganin an samar da ingantaccen ilimi, kuma mafi kyawun ababen more rayuwa a cikin jami’o’i, inji shugaban.

Ya kara da cewa, NLC za ta ci gaba da gudanar da zanga-zangar lumana har sai an magance matsalar ta yadda ya kamata, inda ya jaddada cewa, ma’aikatan ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen shiga cikin kulle-kulle baki daya.

A nasa jawabin, shugaban ASUU na jihar Kebbi, Kwamared Yayale Ibrahim Danjuma,  ya ce “yajin aikin ya zama dole domin kara matsawa gwamnati lamba don ganin ta cika alkawarin da ta dauka.”

Yaa jaddada cewa, jami’o’in na da karancin kayan aikin koyar da dalibai, alhalin albashin malamai ba ya isarsu.

Hakazalika, shugaban kungiyar dalibai a jihar, Muhammed Muhaed Manjo, ya kuma bayyana cewa ilimi hakki ne na dukkan ‘ya’yan Nijeriya, ba gata ba ne, ya jaddada cewa, sun gaji da zama a gidajensu, ya kuma yaba wa ASUU, NLC da suka yi hadin gwiwa don gudanar da zanga-zangar lumana.

 

A sakon shugaban kungiyar NLC ta kasa, wanda ya shugaban kungiyar na jihar Kebbi ya wakilta , Kwamared Alhassa, a yayin gabatar da takardar zanga-zangar ta su ga Gwamna Abubakar Atiku Bagudu, ya yaba wa gwamnan bisa kasancewa cikin gwamnoni biyar da suka biya ‘yan fansho garatuti da biyan albashin ma’aikata a kai a kai da kuma jajircewa wurin jin dadin al’umma a Jihar kebbi.

 

Ya bayyana cewa, sun je gidan gwamnati ne domin gabatar masa da wasikar zanga-zangar su domin ya shiga cikin maganar yajin aikin ASUU, ya jaddada cewa, a matsayinsa na shugaban kungiyar gwamnonin Jam’iyyar APC da ya sa baki don kawo karshen yajin aikin da aka dade ana yi a jami’o’in kasa mu Nijeriya.

A nasa martanin, Glgwamna Abubakar Atiku Bagudu, wanda ya bayyana yajin aikin a matsayin abin damuwa, ya kuma bukaci kungiyoyin kwadago a jihar da su fito da hanyoyin da za a bi domin kawo karshen yajin aikin da kuma yadda za a samar da kudade a fannin ilimi a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUBirnin KebbiKebbiNlcZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaben Fidda-Gwanin PDP: Kotu Ta Fara Sauraren Karar Dan Majalisar Argungu/Augie a Kebbi

Next Post

Harin Kuje: DSS Ta Fitar Da Rahoton Tsaro 44 Kafin Kai Harin – Wase

Related

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

1 month ago
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

2 months ago
Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya
Kananan Labarai

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

3 months ago
Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi

4 months ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Kananan Labarai

Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

9 months ago
Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara
Labarai

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

10 months ago
Next Post
Harin Kuje: DSS Ta Fitar Da Rahoton Tsaro 44 Kafin Kai Harin – Wase

Harin Kuje: DSS Ta Fitar Da Rahoton Tsaro 44 Kafin Kai Harin – Wase

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

June 28, 2025
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

June 28, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.