ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yajin Aikin ‘Yan Kwadago: Yadda Rarrabuwar Kawuna Ta Kawo Cikas

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Kwadago

Rarrabuwar kawuna ta ya haifar da cikas ga samun nasarar yajin aikin gargadi na kungiyar kwadago (NLC) na kwanaki biyu domin matsin lamba ga gwamnatin tarayya ta gaggauta aiwatar da tsare-tsaren rage radadin cire tallafin man fetur.

A duk fadin tarayyar kasar nan kungiyoyin TUC da NLC sun samu rarrabukar kawuna kan yajin aikin da suka shirya tun daga Talata har zuwa Laraba na wan-nan mako.

  • An Samu Nasarori Sama Da 1100 A Gun CIFTIS Na Shekarar 2023
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Jam’iyyar APM Ta Shigar Kan Ingancin Shettima

TUC ta ce tana adawa da yajin aikin ne saboda ba zai haifar da da mai ido ba.

ADVERTISEMENT

A ranar Litinin an rufe dukkan ofishoshin gwamnati da suka hada da ma’aikatu da hukumomi, bayan da ma’aikatan Jihar Kwara suka tsunduma yajin aiki kamar yadda kungiyar NLC ta ba da umarni.

Amma masu zaman kansu sun bude wuraren kasuwancinsu don gudanar da ayyukansu na yau da kullun ba tare da wani tsangwama ba.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Wasu bankunan a Ilorin, babban birnin jihar suma sun gudanar da ayyukansu.

LEADERSHIP ta bayyana cewa, ma’aikatan da aka gani a ofisoshin da ke sakatari-yar jihar su ne ‘yan kungiyar TUC da suka ce ba sa cikin yajin aikin, yayin da sau-ran ma’aikatan da ke karkashin NLC suka rufe suka koma gida gaba daya bisa bin umarnin kungiyar.

A Babban Birnin Tarayya (Abuja) ya samu cikas daga wasu ma’aikatun da kuma hukumomin gwamnati a yajin aikin kwanaki biyu da kungiyar kwadago ta Nijeriya ta ayyana a fadin kasar nan.

A lokacin da LEADERSHIP ta ziyarci sakatariyar gwamnatin tarayya tare da wasu manya-manyan wurare irin su FCTA da FCDA, da kuma wasu bankunan yankin, an gano cewa kadan daga cikin wadannan wuraren suka bi yajin aikin, yayin da wasu kuma ba su bi ba kwata-kwata.

Shugaban kungiyar na Jihar Kuros Ribas, Kwamared Monday Ogbodum, ya yi Al-lah-wadai da yajin aikin gargadi na kwanaki biyu da shugabannin kungiyar NLC suka shiga, inda ya bayyana shugabancin kungiyar a matsayin maras alkimla.

Ogbodum, wanda ya zama shugaban kungiyar manyan ma’aikatan gwamnati a Jihar Kuros Ribas, ya bayyana cewa kungiyar TUC ba ta goyon bayan yajin aikin saboda NLC ba ta bi ka’ida ba kafin ta kira mambobinta da su shiga yajin aikin gargadi na kwanaki biyu, wanda siffanta lamarin da bai cika ka’ida ba.

Shugaban na TUC ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da LEADERSHIP a wata tattaunawa ta wayar tarho a jiya bayan NLC ta bukaci ma’aikatan jihar su zauna a gida.

“Domin bin tsarin da ya dace, mun ware makonni biyu, a yanzu haka muna da wa’adin kwanaki bakwai kafin daga bisani mu umarci ma’aikata su shiga yajin aiki ko kuma akasin haka.

“Muna sane da cewa ‘yan Nijeriya na shan wahala, amma yajin aiki ba shi ne zai kawo mafita ba. TUC ta kasance ‘yan gaba-gaba wajen warware lamarin na tun-karar gwamnatin tarayya.

“Tattaunawa shi ne mafita. Ta hanyar tattaunawa ne shugabannin NLC da TUC da gwamnatin tarayya suka kai wa jahohi tallafin naira biliyan 5. Mun yi maganar gyaran matatun mai, ba zai zama abun da za a iya warwarewa lokaci guda ba. Shugaban kasa ya bayar da sanarwar cewa matatun man za su fara aiki zuwa Dis-amba 2023.

Yajin aikin dai ya samu tangarda a Jihar Legas, yayin da ma’aikatan gwamnati da ma’aikatu masu zaman kansu suka yi watsi da yajin aikin, wanda jama’a sun ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum yadda ya kamata, kamar yadda LEADERSHIP ta bayyana.

Sakamakon binciken da LEADERSHIP ta yi ya nuna cewa yajin aikin ya fi tasiri ga ma’aikatan hukumar da ke kula da bakin teku, domin an hana ma’aikata shiga tashoshin jiragen ruwa, yayin da bankuna da kamfanonin inshora da sauran masu gudanar da aiki a sassan kasar nan suka ci gaba da gudanar da ayyukansu nay au da kullum duk da kokarin talasta musu da wasu ‘yan kungiyar kwadago suka yi domin dakatar da su.

Tun da kiran yajin aikin bai hada da zanga-zangar a kan tituna ba, yajin aiki ne wanda ke nufin ma’aikata gwamnatin tarayya da na jihohi da kuma na kananan hukumomi kar su tafi wuraren aikinsu.

A halin da ake ciki, binciken LEADERSHIP ya ruwaito cewa kofofin shiga Sakatari-yar Alausa da ke Ikeja a Jihar Legas a bude suke kamar yadda aka saba domin shigowar ma’aikata.

Kwadago
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
Next Post
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

An Kama Wasu 'Yansanda Da Laifin Karbar Kudi Da Cin Zarafin Wasu Mutane A Ribas

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.