ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Wasu ‘Yansanda Da Laifin Karbar Kudi Da Cin Zarafin Wasu Mutane A Ribas

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Ribas

Rundunar ‘yansandan Jihar Ribas ta cafke wasu ‘yansanda hudu da ake zargi da cin zarafin wasu mutane uku tare da karbar Naira miliyan 6.5 daga hannunsu.

An ce ‘yan sandan sun cafke mutanen ne ‘yan asalin Omoluwabi da ke Karamar Hukumar Ogba-Egbema-Ndoni ta jihar, ‘yansandan sun batawa mutanen suna ta hanyar kala musu karyar cewa wai ‘yan damfarar intanet ne, inda aka kai su Jihar Delta suka tsare kuma suka kudin daga hannunsu bayan sun tsare su na tsawon kwanaki biyu.

  • Hajjin Badi: Dalilin Kara Kudin Kujera Zuwa Naira Miliyan 4.5 – NAHCON
  • Firaministan Sin Ya Bukaci Taron Kolin Gabashin Asiya Da Ya Inganta Zaman Lafiya Da Wadata A Yankin

An gano cewa ‘yansandan sun kama mutanen ne a ranar 31 ga watan Yuli, 2023, sannan suka sake su a ranar 1 ga Agusta, 2023.

ADVERTISEMENT

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Emeka Nwonyi, yayin da yake gabatar da ‘yansandan a gaban ‘yan jarida a Fatakwal, ya ce yana bakin kokarinsa wajen ganin ya kawar da bara gurbi.

Nwonyi ya ce, “Kuna iya ganin wasu jami’an ‘yansanda. Sama da mako biyu kenan a tsare saboda wani laifi, sun aikata laifin bisa radin kansu, mu kuma mun kama su don mu nuna cewa muna nan kan aikinmu na ganin mun tsarkake kanmu.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

“Ba na jin akwai wata hukuma kamar hukumar ‘yansanda wajen tsaftace al’umma da kokarin fitar da marasa gaskiya daga cikin al’umma a cikin tsari.”

Sai dai shugaban ‘yansandan bai bayyana sunayen ‘yan sandan ba.

Hakazalika, Nwonyi ya gabatar da wasu ‘yansanda hudu da suka hada da Sufetoci uku da aka kama bisa zargin cin zarafin wata dake kan hanyar balaguro.

Ya ce ‘yansandan sun yi ta kai farmaki ne a lokacin da suka yi wa matar fyade a kusa da ‘Arcania Junction’, Ada George Road a Fatakwal ranar Lahadi.

Agba Emmanuel, da wasu mutane uku da suka hada da sufeta Abgani Peter, sufeta Ozenewa Amadi da Sargeant Akuigbo Bartholomew.

“An kama su duka kuma suna tsare ana yi musu tambayoyi.

“Har ila yau, ina kira ga matar da aka ci zarafinta da ta zo ofishina ta ba mu bayanan bangarenta game da lamarin domin a gudanar da bincike mai inganci.”

Ribas
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
NSCDC Ta Kama Barayin Kebur Da Suka Yi Shigar Injiniyoyi A Abuja

NSCDC Ta Kama Barayin Kebur Da Suka Yi Shigar Injiniyoyi A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.