• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Sake Yaduwar Cutar Tarin Fuka

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Yaki Da Sake Yaduwar Cutar Tarin Fuka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kokarin da gwamnatin Nijeriya take na fatattakar cutar tarin fuka (TB) ya ci gaba da samun fuskantar matsaloli. Wani rahoton da aka fitar kwanan nan daga Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ya nuna cewa, kasar nan ce a kan gaba na yawan masu cutar ba yankin Afirka, ita ce kuma ta 6 a jerin kasashe masu fama da cutar a duniya gaba daya.Wannan karin  takaicin kuma shi ne cutar ke kashe ko wane mutum daya a duk minti biyar duk kuwa da cewa ana iya rigakafinta, Kididdiga ta nuna cewa cutar na kashe mutum 97,900 duk shekara a Nijeriya.

Hukumar Lafiya ta Duniya ta nuna matukar damuwarta a kan yadda ake samun karuwar masu fama da cutar a kasar. Ta ci gaba da  nuna damuwar ne saboda Nijeriya ke  da kashi 23 na mace-mace da ake yi a Afrika sanadiyyar cutar Fukar, duk  da tana da cibiyar  kula da masu cutar 50 a fadin kasar,  ana iya samar da hanyoyin kariya na jinyar masu fama da cutar ba tare da wata wahala ba.

  • PSG Ta Shiga Gaban Chelsea Wajen Neman Daukar Victor Osimhen 
  • Sin: An Fitar Da Tsarin Tallafin Kudade Domin Bunkasa Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Idan za a iya tunawa an fara shirin gangamin yaki da cutar fuka da kuturta a Nijeriya (NTBLCP) ne tun a shekarar 1989. Amma kuma wannan kokarin bai haifar da da mai ido ba, musamman ma idan aka yi la’akari da rahottanin da ke shigo wa daga sassan kasa inda suke nuna babu wani ci gaba mai karfafa gwiwa, a daidai lokacin da ake bikin ranar cutar fuka ta duniya an samu rahottanin karuwar yaduwar cutar a tsakanin al’umma.

A duk fadin kasar, labarin daya ne babu jiha ko  ko wata karamar hukumar da ta tsira daga cutar inda take kisa ba kakkautawa.Bayani ya nuna cewa, mutum 7,000 ne suka mutu sanadiyyar kamuwa da cutar a Jihar Kros Ribas kadai. Cutar ta fi kamari ne a kananan hukumomin Kalaba ta Yamma, Ogoja, Boki da kuma Yakurr.

Haka nan ma mutum 7,496 suka kamu da cutar a jihohin Inugu da Borno, yayin da kwamishinan lafiya na Jihar Kwara, Dokta Amina El-Imam, ta bayyana cewa, cutar tarin Fuka ta yi sanadiyyar mutuwar mutum 1,869 a shekarar 2023. Haka kuma kwamishinan Lafiya na Jihar Inugu Farfesa Ikechukwu Obi, ya tabbatar da cewa mutum 2,496 suka kamu da cutar tarin Fuka a jihar a shekarar 2022.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

A shekarar 2023, gwamnatin jihar Borno  ta bakin kwamishinan lafiya na jihar Farfesa Baba Malam-Gana, ta ce an samu masu cutar tarin Fuka 5,000 ana kuma zargin cewa fiye da mutum 10.000 suke dauke da cutar a fadin jihar. Bayanin ya kuma nuna cewa, a Jihar Kano an samu masu fama da cutar har mutum 26,271 a shekarar 2022.A zangon karshe na shekarar 2022, an samu barkewar cutar har sau 9,941 wannan shi ne mafi yawa a tarihin cutar a Nijeriya.

A ra’ayin wannan jaridar, abin takaici ne yadda yawan wadanda cutar ya kashe ma fi yawan wadanda cutar korona ta kashe gaba daya, wannan kuma yana faruwa ne duk da majalisar dinkin duniya ta ayyana shekarar 2030 a matsayin shekarar da za a kawo karshen cutar gaba daya a fadin duniya.

Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana cewa, wani kwayar cutar mai suna ‘mycobacterium tuberculosis bacteria’ ke haifar da cutar tarin fuka, cutar na kai hari huhu ne tana kuma iya shafar wasu sassan jiki gaba daya.

Wani abin mamaki anan shi ne yadda kashi goma na masu fama da cutar basu nuna cikakken alamu amma kuma daga nan sai kaga cutar tana yin ajalin mutum in har ba a dauki matakin da ya kamata ba.

Muna sane da cewa, ko kashi 17 na kudaden da aka ware wa yaki da cutar Fuka baya samun fitowa daga asusun gwamnati. Duk da haka ya kamata cututtuka da ke zama barazana ga rayuwar al’umma kamar cututtukan fuka, maleriya,  kanjamau da sauransu a dauki matakin dakile yaduwar su gaba daya.

A mastayinmu na gidan jarida muna da ra’ayin cewa, wannan shi ne lokacin da ya kamata a kara kaimi wajen yaki da cutar tarin fuka ta hanyar kara hanyoyin fadakar da al’umma illar da hanyoyin kare kai daga kamuwa da ita.

Damuwarmu kuma ita ce al’umma da dama basu san komai ba dangane da cutar da hanyoyin kare kai daga gareta. Wannan yana nuna cewa, dole a karfafa fadakar da al’umma hanyoyin kariya tare da gagauta gano cutar da gaggawa.

Ya kamata gwamnatocin jihohi da sauran masu ruwa da tsaki su hada hannu don yin gangamin yaki da cutar ta hanyar kara zuba kudaden aiki da karfafa malaman lafiya da ke  jinyar masu dauke da cutar. Kungiyoyi masu zaman kansu na da tasu gudunmawar da za su bayar domin samun ita nasarar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Binciken Da Eu Ta Yiwa Wasu Kamfanonin Sin Masu Samar Da Wasu Hajoji

Next Post

Barka Da Sallah: Shugabanni Sun Yi Kiran Amfani Da Darussan Ramadan

Related

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

1 hour ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

21 hours ago
An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

1 day ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

1 day ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

1 day ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

2 days ago
Next Post
Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya

Barka Da Sallah: Shugabanni Sun Yi Kiran Amfani Da Darussan Ramadan

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.