• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Sake Yaduwar Cutar Tarin Fuka

by Leadership Hausa
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Yaki Da Sake Yaduwar Cutar Tarin Fuka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kokarin da gwamnatin Nijeriya take na fatattakar cutar tarin fuka (TB) ya ci gaba da samun fuskantar matsaloli. Wani rahoton da aka fitar kwanan nan daga Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ya nuna cewa, kasar nan ce a kan gaba na yawan masu cutar ba yankin Afirka, ita ce kuma ta 6 a jerin kasashe masu fama da cutar a duniya gaba daya.Wannan karin  takaicin kuma shi ne cutar ke kashe ko wane mutum daya a duk minti biyar duk kuwa da cewa ana iya rigakafinta, Kididdiga ta nuna cewa cutar na kashe mutum 97,900 duk shekara a Nijeriya.

Hukumar Lafiya ta Duniya ta nuna matukar damuwarta a kan yadda ake samun karuwar masu fama da cutar a kasar. Ta ci gaba da  nuna damuwar ne saboda Nijeriya ke  da kashi 23 na mace-mace da ake yi a Afrika sanadiyyar cutar Fukar, duk  da tana da cibiyar  kula da masu cutar 50 a fadin kasar,  ana iya samar da hanyoyin kariya na jinyar masu fama da cutar ba tare da wata wahala ba.

  • PSG Ta Shiga Gaban Chelsea Wajen Neman Daukar Victor Osimhen 
  • Sin: An Fitar Da Tsarin Tallafin Kudade Domin Bunkasa Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Idan za a iya tunawa an fara shirin gangamin yaki da cutar fuka da kuturta a Nijeriya (NTBLCP) ne tun a shekarar 1989. Amma kuma wannan kokarin bai haifar da da mai ido ba, musamman ma idan aka yi la’akari da rahottanin da ke shigo wa daga sassan kasa inda suke nuna babu wani ci gaba mai karfafa gwiwa, a daidai lokacin da ake bikin ranar cutar fuka ta duniya an samu rahottanin karuwar yaduwar cutar a tsakanin al’umma.

A duk fadin kasar, labarin daya ne babu jiha ko  ko wata karamar hukumar da ta tsira daga cutar inda take kisa ba kakkautawa.Bayani ya nuna cewa, mutum 7,000 ne suka mutu sanadiyyar kamuwa da cutar a Jihar Kros Ribas kadai. Cutar ta fi kamari ne a kananan hukumomin Kalaba ta Yamma, Ogoja, Boki da kuma Yakurr.

Haka nan ma mutum 7,496 suka kamu da cutar a jihohin Inugu da Borno, yayin da kwamishinan lafiya na Jihar Kwara, Dokta Amina El-Imam, ta bayyana cewa, cutar tarin Fuka ta yi sanadiyyar mutuwar mutum 1,869 a shekarar 2023. Haka kuma kwamishinan Lafiya na Jihar Inugu Farfesa Ikechukwu Obi, ya tabbatar da cewa mutum 2,496 suka kamu da cutar tarin Fuka a jihar a shekarar 2022.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara ÆŠaya

A shekarar 2023, gwamnatin jihar Borno  ta bakin kwamishinan lafiya na jihar Farfesa Baba Malam-Gana, ta ce an samu masu cutar tarin Fuka 5,000 ana kuma zargin cewa fiye da mutum 10.000 suke dauke da cutar a fadin jihar. Bayanin ya kuma nuna cewa, a Jihar Kano an samu masu fama da cutar har mutum 26,271 a shekarar 2022.A zangon karshe na shekarar 2022, an samu barkewar cutar har sau 9,941 wannan shi ne mafi yawa a tarihin cutar a Nijeriya.

A ra’ayin wannan jaridar, abin takaici ne yadda yawan wadanda cutar ya kashe ma fi yawan wadanda cutar korona ta kashe gaba daya, wannan kuma yana faruwa ne duk da majalisar dinkin duniya ta ayyana shekarar 2030 a matsayin shekarar da za a kawo karshen cutar gaba daya a fadin duniya.

Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana cewa, wani kwayar cutar mai suna ‘mycobacterium tuberculosis bacteria’ ke haifar da cutar tarin fuka, cutar na kai hari huhu ne tana kuma iya shafar wasu sassan jiki gaba daya.

Wani abin mamaki anan shi ne yadda kashi goma na masu fama da cutar basu nuna cikakken alamu amma kuma daga nan sai kaga cutar tana yin ajalin mutum in har ba a dauki matakin da ya kamata ba.

Muna sane da cewa, ko kashi 17 na kudaden da aka ware wa yaki da cutar Fuka baya samun fitowa daga asusun gwamnati. Duk da haka ya kamata cututtuka da ke zama barazana ga rayuwar al’umma kamar cututtukan fuka, maleriya,  kanjamau da sauransu a dauki matakin dakile yaduwar su gaba daya.

A mastayinmu na gidan jarida muna da ra’ayin cewa, wannan shi ne lokacin da ya kamata a kara kaimi wajen yaki da cutar tarin fuka ta hanyar kara hanyoyin fadakar da al’umma illar da hanyoyin kare kai daga kamuwa da ita.

Damuwarmu kuma ita ce al’umma da dama basu san komai ba dangane da cutar da hanyoyin kare kai daga gareta. Wannan yana nuna cewa, dole a karfafa fadakar da al’umma hanyoyin kariya tare da gagauta gano cutar da gaggawa.

Ya kamata gwamnatocin jihohi da sauran masu ruwa da tsaki su hada hannu don yin gangamin yaki da cutar ta hanyar kara zuba kudaden aiki da karfafa malaman lafiya da ke  jinyar masu dauke da cutar. Kungiyoyi masu zaman kansu na da tasu gudunmawar da za su bayar domin samun ita nasarar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bayyana Rashin Jin Dadi Kan Binciken Da Eu Ta Yiwa Wasu Kamfanonin Sin Masu Samar Da Wasu Hajoji

Next Post

Barka Da Sallah: Shugabanni Sun Yi Kiran Amfani Da Darussan Ramadan

Related

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

13 hours ago
Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara ÆŠaya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Tsawaita Wa’adin Shugaban Kwastan Da Shekara ÆŠaya

14 hours ago
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC

20 hours ago
Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya

23 hours ago
Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

2 days ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

2 days ago
Next Post
Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya

Barka Da Sallah: Shugabanni Sun Yi Kiran Amfani Da Darussan Ramadan

LABARAI MASU NASABA

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

July 31, 2025
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

July 31, 2025
NIN-SIM: Masu Hulda Da Kamfanonin Sadarwa Sun Koka Kan Katse Layinsu Daga Tsarin Kira

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

July 31, 2025
Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

July 31, 2025
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

July 31, 2025
Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

July 31, 2025
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

July 31, 2025
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

July 31, 2025
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

July 31, 2025
Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.