• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaki Da Talauci: Yadda Kasar Sin Ke Taka Rawar Gani A Duniya 

by Sulaiman
9 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Yaki Da Talauci: Yadda Kasar Sin Ke Taka Rawar Gani A Duniya 

лªÉçÕÕÆ¬£¬ËçµÂ³£¨Àû±ÈÀïÑÇ£©£¬2015Äê11ÔÂ12ÈÕ £¨¹ú¼Ê¡¤Í¼ÎÄ»¥¶¯£©£¨5£©·ÇÖÞÃÜÁÖÀ´ÁËÖйú¡°°×Çó¶÷¡± 11ÔÂ1ÈÕ£¬ÔÚÀû±ÈÀïÑÇËçµÂ³Êи½½ü´åׯ£¬µ±µØ´åÃñÅŶӽÓÊÜÖйúµÚ18Åú¸°Àû±ÈÀïÑÇάºÍ²¿¶ÓÒ½ÁÆ·Ö¶ÓÒåÕï¡£ ËçµÂ³ÊÇÀû±ÈÀïÑǵڶþ´ó³ÇÊУ¬µ«ÊÐÇø¾ÍºáÊúÁ½ÌõÂí·£¬Ê®¼¸ÍòÈ˿ڴó¶àÉ¢¾ÓÔÚԭʼɭÁÖÖлòÂí·Á½±ßµÄ·¿ÎÝÀï¡£×Ô12Äêǰ²Î¼ÓÁªºÏ¹úÔÚÀû±ÈÀïÑÇάºÍÈÎÎñÒÔÀ´£¬ÖйúפÀû±ÈÀïÑÇάºÍ²¿¶Ó¹¤±ø·Ö¶ÓºÍÒ½ÁÆ·Ö¶ÓµÄÓªµØ¾ÍÒ»Ö±ÉèÔÚÕâÀÁ½¸öÓªµØ¶¼ÊÇÓÃËÜÁϰåÁÙʱ´î½¨£¬·Ç³£¼òª¡£ лªÉç¼ÇÕßËïÈð²©Éã

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Talauci babbar barazana ne ga ci gaban dan Adam ganin har yanzu akalla mutane biliyan daya na cikin matsanancin talauci a duniya. Bari mu duba yadda kasar Sin ke samar da turba mai kyakkyawan fata ga samun ingantacciyar rayuwa.

 

Kasar Sin ta yi nasarar tsame mutane miliyan 800 daga kangin talauci tare da cimma burin rage radadin talauci bisa ajandar ci gaba mai dorewa ta Majalisar Dinkin Duniya ta 2030 tun kafin lokacin da aka tanada. Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres da kansa, ya yabawa nasarar da kasar Sin ta samu a matsayin “Nasarar yaki da kangin talauci mafi girma a tarihi”.

  • Minista Ya Buƙaci Sabbin Shugabannin NIPR Su Faɗakar da Jama’a Yadda Ya Dace 
  • An Yi Wa Shugaban Ƙasar Brazil Lula Da Silva Tiyatar Ƙwaƙwalwa 

Dabarun rage talauci na kasar Sin sun kuma taimaka ga daidaita kalubalen talauci da sauran kasashen duniya ke fuskanta.

 

Labarai Masu Nasaba

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

Misali, ta hanyar manufofi irin su shawarar “ziri daya da hanya daya”, kasar Sin tana aiki da kasashe masu tasowa a duk duniya wajen samar da ayyukan more rayuwa, ilimi da kiwon lafiya. Wanda hakan ya fitar da miliyoyi daga talauci.

 

Haka nan kasar Sin ta yi matukar tasiri ga ci gaban tattalin arzikin Nijeriya ta hanyoyi da dama, domin ita ce babbar abokiyar cinikayyar Nijeriya. Sin ta zama babbar hanyar zuba jari ta kai tsaye daga ketare (FDI) a Nijeriya, musamman a fannin ababen more rayuwa, hakar ma’adinai, da sadarwa.

 

Baya ga fasahar kere-kere, da fasahohin ilmi ga masana’antun Nijeriya da kamfanonin Sin suka taimaka da kasar da ita, har ila yau kasar Sin ta taimaka wajen gina hanyoyin jirgin kasa kamar na Abuja zuwa Kaduna, da Legas zuwa Ibadan. Kamfanonin kasar Sin sun kuma gina tasoshin samar wutar lantarki, da hanyoyin sadarwa, da ayyukan sabunta makamashi daban-daban a Nijeriya.

 

Zuwa yanzu, kasar Sin ta ba da taimakon raya kasa ga kasashe sama da 160, ta yi hadin gwiwa mai inganci na tsarin “ziri daya da hanya daya” tare da kasashe sama da 150, ta kuma tallafa wa ayyukan more rayuwa sama da 1,100 da kusan dalar Amurka biliyan 20 na tallafin raya kasa.

 

Gudunmawar da kasar Sin ta bayar wajen yaki da kangin talauci a duniya, bai tsaya kan bayar da taimakon kudi da fasaha kadai ba domin ta kuma horar da kwararru sama da 400,000 daga kasashe da yankuna sama da 180, tare da karfafa kokarinsu na kawar da fatara.

 

A wurin taron kolin G20 da aka kammala kwanan nan a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil, shugaban kasar Sin, Xi Jinping ya jaddada matakai takwas da kasar Sin za ta dauka na taimaka wa raya kasa da kasa musamman ga kasashe masu karamin karfi. Duk wadannan sun sa kasashe masu tasowa amincewa da kasar Sin a matsayin amintacciyar abokiyar hulda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Minista Ya Buƙaci Sabbin Shugabannin NIPR Su Faɗakar da Jama’a Yadda Ya Dace 

Next Post

An Gabatar Da Ci Gaban Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa a Cop16 Kan Hana Kwararar Hamada

Related

Fyade
Ra'ayinmu

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

1 week ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Ra'ayinmu

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

2 weeks ago
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu
Ra'ayi Riga

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

3 weeks ago
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye
Ra'ayi Riga

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

4 weeks ago
Ra'ayinmu

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

2 months ago
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)
Ra'ayinmu

Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta

2 months ago
Next Post
An Gabatar Da Ci Gaban Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa a Cop16 Kan Hana Kwararar Hamada

An Gabatar Da Ci Gaban Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa a Cop16 Kan Hana Kwararar Hamada

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta Farfaɗo Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

Sin Da Amurka Sun Fara Gudanar Da Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Madrid

September 14, 2025
An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

An Gano Gawar Yarinyar da Ruwan Sama Ya Tafi Da ita A Zariya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.