Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

’Yan Arewa 2,056 Za Su Amfana Da Tallafin Karatu Daga NEDC Na Biliyan Shida

by Muhammad
December 30, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Tallafin Karatu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya,

Hukumar bunkasa shiyyar arewa maso gabas (NEDC) ta bayyana a jiya cewa mutane dubu biyu da hamsin da shida (2,056) ne za su amfana da tallafin biliyan shida (6bn) a karkashin shirin hukumar na tallafa wa jama’a kan harkokin ilimi wato (NEDC-EEF).
A sanarwar manema labarai da jami’in hulda da jama’a na hukumar Abba Musa ya fitar, ya shaida cewar mutum 2,056 za su samu tallafin karatu kyauta a manyan jami’o’i a karkashin wannan kudin.
An samar da hukumar ne dai da zummar farfado da shiyyar arewa maso gabas bayan da ‘yan ta’addan Boko haram suka daidaya shiyyar.
Da ya ke bayani kan nasarorin da suka cimma kuwa, ya shaida cewar sun jima suna tallafa wa marayu da masa karfi, kana a cikin wannan kudin ma marayu da makara galihu za su amfana sosai.
“Tallafin karatun da aka ware din zai hada da daliban jami’a masu neman digiri, da masu neman digiri na biyu, da kuma masu digiri na uku, da za a tsakulo daga jihohin arewa maso gabas. Dalibai 2,056 daga gundumomi 1,028 da ke arewa maso gabas ne za su amfana da wannan tallafin.
Kan nasarorin da suka cimma tun bayan da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da hukumar a 2019 a karkashin jagorancin Janar Pau Talfa (ritaya) da Mohammed Alkali, sun samu nasarar gudanar da ayyukan jinya kyauta ga marasa lafiya da daman gaske.
Ya ce, daga cikin marasa lafiyan da hukumar ta dauki nauyi har da tiyata da sauran muhimman fannoni da aka taimaka wa majinyata dubbai.
Ya ce, ko bayan barkewar annobar Korona hukumar ta taimaka wa gwamnatocin shiyyar da dama wajen samar musu da kayyakin kula da lafiya da rage yaduwar cutar domin dakilewa tare da kariya, inda yake mai cewa sun gudanar da muhimman ayyuka na tallafi dukka a kokarin hukumar na farfado da shiyyar arewa maso gabas.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Korona Ta Sake Kashe 10, Ta Kama 397 A Nijeriya Shekaranjiya

Next Post

Mu Na Alfahari Da Bin Jagorancin Kwankwaso – Ibrahim Ali Namadi

RelatedPosts

Sojoji Sun Tarwatsa Sansanin Boko Haram A Borno 

by Sulaiman Ibrahim
6 hours ago
0

Rundunar sojan Najeriya ta bayyana samun nasarar tarwatsa sansanin da...

Jam'iyyar Adawa

Jam’iyyar Adawa Ta PDP Ta Yi Babban Kamu A Kebbi

by Sulaiman Ibrahim
6 hours ago
0

Jam'iyyar adawa ta PDP a jihar Kebbi tayi babban kamu...

Majalisar Malamai

Majalisar Malamai A Kogi Ta Raba Zakkar Miliyan N2.5 Ga Mutum 63

by Sulaiman Ibrahim
6 hours ago
0

Majalisar Malamai ta Najeriya,reshen jihar Kogi(Council of Ulama) ta rarraba...

Next Post
Jagorancin

Mu Na Alfahari Da Bin Jagorancin Kwankwaso – Ibrahim Ali Namadi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version