• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yan Bindiga Na Ci Gaba Da Addabar Arewa Maso Yamma

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
 ‘Yan Bindiga Na Ci Gaba Da Addabar Arewa Maso Yamma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan bindiga na ci gaba da addabar arewa maso yammacin Nijeriya, al’amarin da ke daidaita al’ummar yankin duk da jami’an tsaro na samun galaba a kansu kamar yadda rundunonin tsaro suka sha bayyanawa.

Al’ummomin kauyuka 10 da suke karamar hukumar Giwa ta Jihar Kaduna sun tsere, inda suka bar gidajensu domin tsira da rayukansu sakamakon aikace-aikacen ‘yan fashin daji da suka addabi yanki.

  • Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh
  • Za A Fara Amfani Da Sabon Layin Jirgin Ƙasa Na Dakon Kaya Daga Legas Zuwa Kano A Watan Gobe

An tattaro cewa wadanda lamarin ya fi shafa mata ne da yara, sun yi tattaki na tsawon zango domin neman wurin da za su yi gudun hijira a cikin babban garin Giwa.

Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Giwa ta yamma a majalisar dokokin Jihar Kaduna, Umar Auwal Bijimi ya shaida wa majiyarmu cewa tashin hankalin ya faru ne tun lokacin da aka janye jajirtaccen soja, Sajet Usman Hamisu Bagobiri, wanda ya ba da gagarumin gudummuwa wajen dakile motsin ‘yan fashin daji a yankin.

Ya ce, rashin kasancewar Sajet Bagobiri a yankin ya bai wa masu aikata laifuka kwarin guiwar ci gaba da tsula tsiyarsu, lamarin da ya janyo jama’a na neman tsira da rayukansu daga kauyuka da daman gaske.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Ya nuna damuwarsa kan garkuwa da mutane na baya-bayan nan da aka yi, musamman na mata, lamarin da ya sanya al’ummomin yankin yanke hukuncin barin gidajensu.

Bijimi ya ce, yankunan da abun ya sha sun hada da Gogi, Angwar Bako, Marge, Tunburku, Bataro, Kayawa da kuma Yuna.

Ya roki gwamnatin jihar da rundunar sojin Nijeriya da su sake dawo da Sajen Bagobiri yankin shi da sauran sojoji masu azamar taimaka wa yankin wajen ganin an kare jama’an yankin daga ‘yan fashin daji, da tabbatar da kare rayuka da dukiyar al’umma domin ganin sun koma gudanar da harkokin nomansu yadda ya kamata.

Sarkin Fatika, Nuhu Lawal Umar ya yi kira da a samar da tsaro a yankin, yana mai cewa yankin na matukar bukatar agajin gwamnati cikin gaggawa.

Kwamishinan tsaron cikin gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan ya ce masu ruwa da tsaki ciki har da shugaban karamar hukumar Giwa, Alhaji Abubakar Shehu Giwa, da shugabannin al’umma sun zauna domin gaggauna yadda za a kyautata lamarin tsaro a yankin.

Ya tabbatar da cewa ana kan kokarin ganin an kawo karshen matsalar tsaron yankin kuma tuni aka dauki matakan inganta samun bayanan sirri da kyautata matakan tsaro a wadannan yankunan.

Haka zalika, ‘Yan bindiga sun kashe mutane takwas tare da yin awon gaba da manajan bankin Taj, Mandir Laura a Jihar Zamfara.

LEADERSHIP ta gano cewa ‘yan bindigar da ke dauke da makamai, wadanda adadinsu ya kai kimanin 15 sun mamaye gidan manajan bankin da ke yankin

Rijiyar Gabas a daren ranar Litinin, inda suka yi awon gaba da shi.

A wani harin na daban, ‘yan bindiga sun kai hari garin Faru da ke karamar hukumar Maradun a jihar, inda suka kashe mutane takwas.

Wasu daga cikin mazauna yankin sun ce ‘yan bindigar sun yi wa yankin kawanya kafin su kaddamar da harin nasu.

Majiyoyin sun kuma kara da cewa an sace mutane tare da tafiya da su cikin daji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Arewa Maso YammaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Biya Wa Ɗalibai 1,740 Kuɗin Makaranta A Jami’ar Ilimi Ta Sa’adatu Rimi

Next Post

Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

2 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

2 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

3 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

3 weeks ago
Next Post
Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

LABARAI MASU NASABA

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

Likitoci Sun Fara Yajin Aikin Gargaɗi Na Mako Ɗaya A Abuja

September 8, 2025
Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

Sanata Natasha Zata Dawo Aiki Bayan Dakatarwar Wata Shida

September 8, 2025
Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

Xi Zai Halarci Taron Kolin Shugabannin Kasashen BRICS Ta Kafar Bidiyo

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

September 7, 2025
Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.