ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yan Bindiga Na Ci Gaba Da Addabar Arewa Maso Yamma

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Arewa

‘Yan bindiga na ci gaba da addabar arewa maso yammacin Nijeriya, al’amarin da ke daidaita al’ummar yankin duk da jami’an tsaro na samun galaba a kansu kamar yadda rundunonin tsaro suka sha bayyanawa.

Al’ummomin kauyuka 10 da suke karamar hukumar Giwa ta Jihar Kaduna sun tsere, inda suka bar gidajensu domin tsira da rayukansu sakamakon aikace-aikacen ‘yan fashin daji da suka addabi yanki.

  • Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh
  • Za A Fara Amfani Da Sabon Layin Jirgin Ƙasa Na Dakon Kaya Daga Legas Zuwa Kano A Watan Gobe

An tattaro cewa wadanda lamarin ya fi shafa mata ne da yara, sun yi tattaki na tsawon zango domin neman wurin da za su yi gudun hijira a cikin babban garin Giwa.

ADVERTISEMENT

Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Giwa ta yamma a majalisar dokokin Jihar Kaduna, Umar Auwal Bijimi ya shaida wa majiyarmu cewa tashin hankalin ya faru ne tun lokacin da aka janye jajirtaccen soja, Sajet Usman Hamisu Bagobiri, wanda ya ba da gagarumin gudummuwa wajen dakile motsin ‘yan fashin daji a yankin.

Ya ce, rashin kasancewar Sajet Bagobiri a yankin ya bai wa masu aikata laifuka kwarin guiwar ci gaba da tsula tsiyarsu, lamarin da ya janyo jama’a na neman tsira da rayukansu daga kauyuka da daman gaske.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Ya nuna damuwarsa kan garkuwa da mutane na baya-bayan nan da aka yi, musamman na mata, lamarin da ya sanya al’ummomin yankin yanke hukuncin barin gidajensu.

Bijimi ya ce, yankunan da abun ya sha sun hada da Gogi, Angwar Bako, Marge, Tunburku, Bataro, Kayawa da kuma Yuna.

Ya roki gwamnatin jihar da rundunar sojin Nijeriya da su sake dawo da Sajen Bagobiri yankin shi da sauran sojoji masu azamar taimaka wa yankin wajen ganin an kare jama’an yankin daga ‘yan fashin daji, da tabbatar da kare rayuka da dukiyar al’umma domin ganin sun koma gudanar da harkokin nomansu yadda ya kamata.

Sarkin Fatika, Nuhu Lawal Umar ya yi kira da a samar da tsaro a yankin, yana mai cewa yankin na matukar bukatar agajin gwamnati cikin gaggawa.

Kwamishinan tsaron cikin gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan ya ce masu ruwa da tsaki ciki har da shugaban karamar hukumar Giwa, Alhaji Abubakar Shehu Giwa, da shugabannin al’umma sun zauna domin gaggauna yadda za a kyautata lamarin tsaro a yankin.

Ya tabbatar da cewa ana kan kokarin ganin an kawo karshen matsalar tsaron yankin kuma tuni aka dauki matakan inganta samun bayanan sirri da kyautata matakan tsaro a wadannan yankunan.

Haka zalika, ‘Yan bindiga sun kashe mutane takwas tare da yin awon gaba da manajan bankin Taj, Mandir Laura a Jihar Zamfara.

LEADERSHIP ta gano cewa ‘yan bindigar da ke dauke da makamai, wadanda adadinsu ya kai kimanin 15 sun mamaye gidan manajan bankin da ke yankin

Rijiyar Gabas a daren ranar Litinin, inda suka yi awon gaba da shi.

A wani harin na daban, ‘yan bindiga sun kai hari garin Faru da ke karamar hukumar Maradun a jihar, inda suka kashe mutane takwas.

Wasu daga cikin mazauna yankin sun ce ‘yan bindigar sun yi wa yankin kawanya kafin su kaddamar da harin nasu.

Majiyoyin sun kuma kara da cewa an sace mutane tare da tafiya da su cikin daji.

Arewa
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.