ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yan Bindiga Na Ci Gaba Da Addabar Arewa Maso Yamma

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Arewa

‘Yan bindiga na ci gaba da addabar arewa maso yammacin Nijeriya, al’amarin da ke daidaita al’ummar yankin duk da jami’an tsaro na samun galaba a kansu kamar yadda rundunonin tsaro suka sha bayyanawa.

Al’ummomin kauyuka 10 da suke karamar hukumar Giwa ta Jihar Kaduna sun tsere, inda suka bar gidajensu domin tsira da rayukansu sakamakon aikace-aikacen ‘yan fashin daji da suka addabi yanki.

  • Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh
  • Za A Fara Amfani Da Sabon Layin Jirgin Ƙasa Na Dakon Kaya Daga Legas Zuwa Kano A Watan Gobe

An tattaro cewa wadanda lamarin ya fi shafa mata ne da yara, sun yi tattaki na tsawon zango domin neman wurin da za su yi gudun hijira a cikin babban garin Giwa.

ADVERTISEMENT

Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Giwa ta yamma a majalisar dokokin Jihar Kaduna, Umar Auwal Bijimi ya shaida wa majiyarmu cewa tashin hankalin ya faru ne tun lokacin da aka janye jajirtaccen soja, Sajet Usman Hamisu Bagobiri, wanda ya ba da gagarumin gudummuwa wajen dakile motsin ‘yan fashin daji a yankin.

Ya ce, rashin kasancewar Sajet Bagobiri a yankin ya bai wa masu aikata laifuka kwarin guiwar ci gaba da tsula tsiyarsu, lamarin da ya janyo jama’a na neman tsira da rayukansu daga kauyuka da daman gaske.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Ya nuna damuwarsa kan garkuwa da mutane na baya-bayan nan da aka yi, musamman na mata, lamarin da ya sanya al’ummomin yankin yanke hukuncin barin gidajensu.

Bijimi ya ce, yankunan da abun ya sha sun hada da Gogi, Angwar Bako, Marge, Tunburku, Bataro, Kayawa da kuma Yuna.

Ya roki gwamnatin jihar da rundunar sojin Nijeriya da su sake dawo da Sajen Bagobiri yankin shi da sauran sojoji masu azamar taimaka wa yankin wajen ganin an kare jama’an yankin daga ‘yan fashin daji, da tabbatar da kare rayuka da dukiyar al’umma domin ganin sun koma gudanar da harkokin nomansu yadda ya kamata.

Sarkin Fatika, Nuhu Lawal Umar ya yi kira da a samar da tsaro a yankin, yana mai cewa yankin na matukar bukatar agajin gwamnati cikin gaggawa.

Kwamishinan tsaron cikin gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan ya ce masu ruwa da tsaki ciki har da shugaban karamar hukumar Giwa, Alhaji Abubakar Shehu Giwa, da shugabannin al’umma sun zauna domin gaggauna yadda za a kyautata lamarin tsaro a yankin.

Ya tabbatar da cewa ana kan kokarin ganin an kawo karshen matsalar tsaron yankin kuma tuni aka dauki matakan inganta samun bayanan sirri da kyautata matakan tsaro a wadannan yankunan.

Haka zalika, ‘Yan bindiga sun kashe mutane takwas tare da yin awon gaba da manajan bankin Taj, Mandir Laura a Jihar Zamfara.

LEADERSHIP ta gano cewa ‘yan bindigar da ke dauke da makamai, wadanda adadinsu ya kai kimanin 15 sun mamaye gidan manajan bankin da ke yankin

Rijiyar Gabas a daren ranar Litinin, inda suka yi awon gaba da shi.

A wani harin na daban, ‘yan bindiga sun kai hari garin Faru da ke karamar hukumar Maradun a jihar, inda suka kashe mutane takwas.

Wasu daga cikin mazauna yankin sun ce ‘yan bindigar sun yi wa yankin kawanya kafin su kaddamar da harin nasu.

Majiyoyin sun kuma kara da cewa an sace mutane tare da tafiya da su cikin daji.

Arewa
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

LABARAI MASU NASABA

Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya

Mulkin Tinubu A Shekara 3:Ina Aka Fito? Ina Aka Dosa?

June 5, 2026
Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

Hajji 2026: Mahajjata 1,905 Sun Dawo Nijeriya Daga Saudiyya

June 5, 2026
Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

June 5, 2026
Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.