ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

 ‘Yan Bindiga Na Ci Gaba Da Addabar Arewa Maso Yamma

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Arewa

‘Yan bindiga na ci gaba da addabar arewa maso yammacin Nijeriya, al’amarin da ke daidaita al’ummar yankin duk da jami’an tsaro na samun galaba a kansu kamar yadda rundunonin tsaro suka sha bayyanawa.

Al’ummomin kauyuka 10 da suke karamar hukumar Giwa ta Jihar Kaduna sun tsere, inda suka bar gidajensu domin tsira da rayukansu sakamakon aikace-aikacen ‘yan fashin daji da suka addabi yanki.

  • Abubuwa Uku Da Za A Yi Farashin Kaya Ya Sauka A Nijeriya – Dakta Saleh
  • Za A Fara Amfani Da Sabon Layin Jirgin Ƙasa Na Dakon Kaya Daga Legas Zuwa Kano A Watan Gobe

An tattaro cewa wadanda lamarin ya fi shafa mata ne da yara, sun yi tattaki na tsawon zango domin neman wurin da za su yi gudun hijira a cikin babban garin Giwa.

ADVERTISEMENT

Dan majalisar da ke wakiltar mazabar Giwa ta yamma a majalisar dokokin Jihar Kaduna, Umar Auwal Bijimi ya shaida wa majiyarmu cewa tashin hankalin ya faru ne tun lokacin da aka janye jajirtaccen soja, Sajet Usman Hamisu Bagobiri, wanda ya ba da gagarumin gudummuwa wajen dakile motsin ‘yan fashin daji a yankin.

Ya ce, rashin kasancewar Sajet Bagobiri a yankin ya bai wa masu aikata laifuka kwarin guiwar ci gaba da tsula tsiyarsu, lamarin da ya janyo jama’a na neman tsira da rayukansu daga kauyuka da daman gaske.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Ya nuna damuwarsa kan garkuwa da mutane na baya-bayan nan da aka yi, musamman na mata, lamarin da ya sanya al’ummomin yankin yanke hukuncin barin gidajensu.

Bijimi ya ce, yankunan da abun ya sha sun hada da Gogi, Angwar Bako, Marge, Tunburku, Bataro, Kayawa da kuma Yuna.

Ya roki gwamnatin jihar da rundunar sojin Nijeriya da su sake dawo da Sajen Bagobiri yankin shi da sauran sojoji masu azamar taimaka wa yankin wajen ganin an kare jama’an yankin daga ‘yan fashin daji, da tabbatar da kare rayuka da dukiyar al’umma domin ganin sun koma gudanar da harkokin nomansu yadda ya kamata.

Sarkin Fatika, Nuhu Lawal Umar ya yi kira da a samar da tsaro a yankin, yana mai cewa yankin na matukar bukatar agajin gwamnati cikin gaggawa.

Kwamishinan tsaron cikin gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan ya ce masu ruwa da tsaki ciki har da shugaban karamar hukumar Giwa, Alhaji Abubakar Shehu Giwa, da shugabannin al’umma sun zauna domin gaggauna yadda za a kyautata lamarin tsaro a yankin.

Ya tabbatar da cewa ana kan kokarin ganin an kawo karshen matsalar tsaron yankin kuma tuni aka dauki matakan inganta samun bayanan sirri da kyautata matakan tsaro a wadannan yankunan.

Haka zalika, ‘Yan bindiga sun kashe mutane takwas tare da yin awon gaba da manajan bankin Taj, Mandir Laura a Jihar Zamfara.

LEADERSHIP ta gano cewa ‘yan bindigar da ke dauke da makamai, wadanda adadinsu ya kai kimanin 15 sun mamaye gidan manajan bankin da ke yankin

Rijiyar Gabas a daren ranar Litinin, inda suka yi awon gaba da shi.

A wani harin na daban, ‘yan bindiga sun kai hari garin Faru da ke karamar hukumar Maradun a jihar, inda suka kashe mutane takwas.

Wasu daga cikin mazauna yankin sun ce ‘yan bindigar sun yi wa yankin kawanya kafin su kaddamar da harin nasu.

Majiyoyin sun kuma kara da cewa an sace mutane tare da tafiya da su cikin daji.

Arewa
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026
Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026
Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.