ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

by Leadership Hausa
2 years ago
Zargin

Kwamishiniyar Mata, Yara da Nakasassu ta Jihar Kano, Aisha Saji ta shiga tsakani kan wasu yara masu kankantar shekaru da ake zargin abokin mahaifinsu ya yi lalata da su domin tabbatar da adalci ga wadanda lamarin ya shafa.

Wata sanarwa da Daraktar Wayar da Kan Jama’a ta Ma’aikatar, Aishatu Haruna, wacce ta ba wa LEADERSHIP kwafinta, ta bayyana cewa kwamishiniyar ta dauki nauyin lamarin ne jim kadan bayan an yada labarin a wani shirin gidan rediyon ‘Yanchi da Rayuwa’.

  • An Samu Sabuwar Damar Kyautata Hulda Tsakanin Sin Da Hungary
  • Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

 Nan take Kwamishiniyar ta umurci daraktoci biyu da kwararrun ma’aikata da su tuntubi wadanda abin ya shafa tare da ba ta ra’ayi.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, yayin ganawa da daya daga cikin wadanda abin ya shafa da mahaifiyarsa a ofishinta, kwamishiniyar ta nuna kaduwarta matuka da jin irin wannan mummunan aiki da aka aikata ga yaro dan shekara takwas da ya kai ga lalata masa dubura.

Bisa la’akari da halin da mutanen da lamarin ya shafa suka shiga, Saji ta yi alkawarin bin diddigin lamarin har zuwa karshe, sannan kuma ya yi kokarin ganin an samar da wata kafa ta gwamnati da za ta samu nasara a shari’a.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Ta kuma yi tayin biyan basussukan da aka tara na tsawon watanni ana jinyar wadanda abin ya shafa, wadanda har yanzu ba su samu cikakkiyar lafiya daga raunukan da suka samu na dubura ba, sannan ta kara tallafa wa dangin da kyautar tufafi da kudi da buhun shinkafa da masara.

Da take magana tun da farko, mahaifiyar wadanda lamarin ya shafa ta ce tsohon mijinta ne ya sanar da ita lamarin inda ya janye karar kuma ya lallashe ta da ta bar batun kai karar, amma ta yanke shawarar sake bude maganar shari’ar ta hanyar ‘yansanda, sannan ta kai kotu. An bayar da belin wadda ake zargin duk da hujjojin da likitan da ya bayar game da ‘ya’yanta.

Ta kuma kara da cewa, a wata ziyarar jinya, wani likita ya fitar da tsutsotsi da suka taru a duburarsu, ya yi wa yaran dinki a duburarsu lamarin da ya sanya shi zubar da hawaye yayin da dayan da abin ya shafa ya rika gudawa babu kakkautawa.

Sai dai mahaifiyar ta ce, duk da cewa an shigar da karar a gaban kotu, amma har yanzu ba a kira su gaban alkali ba.

A nasu jawabansu na daban, wadanda abin ya shafa ‘yan shekaru takwas zuwa goma sun ce wadanda ake zargin sun yi lalata da su ne ta hanyar yi musu barazanar cutar da su idan sun gaya wa wani irin cin zarafin da aka yi musu.

Sai dai sun bayyana cewa duk da wannan barazanar sun kai rahoton lamarin ga mahaifin nasu wanda ya bukaci su yi shiru tare da gargadar su da su boye maganar.

Zargin
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Sarkin Gaya Zai Yi Bikin Naɗin Munzir Yusuf Ali Sabon Sarkin Malamai Ranar Juma’a

Sarkin Gaya Zai Yi Bikin Naɗin Munzir Yusuf Ali Sabon Sarkin Malamai Ranar Juma’a

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.