ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Luwadi: Kwamishiniya A Jihar Kano Ta Sha Alwashin Tabbatar Da Adalci Ga Yaran Da Aka Lalata

by Leadership Hausa
2 years ago
Zargin

Kwamishiniyar Mata, Yara da Nakasassu ta Jihar Kano, Aisha Saji ta shiga tsakani kan wasu yara masu kankantar shekaru da ake zargin abokin mahaifinsu ya yi lalata da su domin tabbatar da adalci ga wadanda lamarin ya shafa.

Wata sanarwa da Daraktar Wayar da Kan Jama’a ta Ma’aikatar, Aishatu Haruna, wacce ta ba wa LEADERSHIP kwafinta, ta bayyana cewa kwamishiniyar ta dauki nauyin lamarin ne jim kadan bayan an yada labarin a wani shirin gidan rediyon ‘Yanchi da Rayuwa’.

  • An Samu Sabuwar Damar Kyautata Hulda Tsakanin Sin Da Hungary
  • Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

 Nan take Kwamishiniyar ta umurci daraktoci biyu da kwararrun ma’aikata da su tuntubi wadanda abin ya shafa tare da ba ta ra’ayi.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar, yayin ganawa da daya daga cikin wadanda abin ya shafa da mahaifiyarsa a ofishinta, kwamishiniyar ta nuna kaduwarta matuka da jin irin wannan mummunan aiki da aka aikata ga yaro dan shekara takwas da ya kai ga lalata masa dubura.

Bisa la’akari da halin da mutanen da lamarin ya shafa suka shiga, Saji ta yi alkawarin bin diddigin lamarin har zuwa karshe, sannan kuma ya yi kokarin ganin an samar da wata kafa ta gwamnati da za ta samu nasara a shari’a.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Ta kuma yi tayin biyan basussukan da aka tara na tsawon watanni ana jinyar wadanda abin ya shafa, wadanda har yanzu ba su samu cikakkiyar lafiya daga raunukan da suka samu na dubura ba, sannan ta kara tallafa wa dangin da kyautar tufafi da kudi da buhun shinkafa da masara.

Da take magana tun da farko, mahaifiyar wadanda lamarin ya shafa ta ce tsohon mijinta ne ya sanar da ita lamarin inda ya janye karar kuma ya lallashe ta da ta bar batun kai karar, amma ta yanke shawarar sake bude maganar shari’ar ta hanyar ‘yansanda, sannan ta kai kotu. An bayar da belin wadda ake zargin duk da hujjojin da likitan da ya bayar game da ‘ya’yanta.

Ta kuma kara da cewa, a wata ziyarar jinya, wani likita ya fitar da tsutsotsi da suka taru a duburarsu, ya yi wa yaran dinki a duburarsu lamarin da ya sanya shi zubar da hawaye yayin da dayan da abin ya shafa ya rika gudawa babu kakkautawa.

Sai dai mahaifiyar ta ce, duk da cewa an shigar da karar a gaban kotu, amma har yanzu ba a kira su gaban alkali ba.

A nasu jawabansu na daban, wadanda abin ya shafa ‘yan shekaru takwas zuwa goma sun ce wadanda ake zargin sun yi lalata da su ne ta hanyar yi musu barazanar cutar da su idan sun gaya wa wani irin cin zarafin da aka yi musu.

Sai dai sun bayyana cewa duk da wannan barazanar sun kai rahoton lamarin ga mahaifin nasu wanda ya bukaci su yi shiru tare da gargadar su da su boye maganar.

Zargin
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Sarkin Gaya Zai Yi Bikin Naɗin Munzir Yusuf Ali Sabon Sarkin Malamai Ranar Juma’a

Sarkin Gaya Zai Yi Bikin Naɗin Munzir Yusuf Ali Sabon Sarkin Malamai Ranar Juma’a

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.