Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

’Yan Bindiga Sun Halaka Mutum Biyar A Binuwai

by Muhammad
December 28, 2020
in RIGAR 'YANCI
1 min read
Ebonyi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya,

 

samndaads

Mutum biyar ne aka bada rahoton kisan su wanda wasu ‘yan bindiga dadi suka aikata da safiyar jiya Lahadi a wasu hari daban-daban da suka faru a kananan hukumomi biyu na jihar Benuwai.

Majiyarmu ta nakalto cewa uku daga cikin wadanda aka kashen masu bindigan sun kutsa kai cikin gidan Inna Jato wani tsohon dan majalisar jihar mai wakiltar mazabar Kastina-Ala ta gabas da ke kauyen Nagu a karamar hukumar Kastina-Ala ta jihar.

Ganau sun shaida cewa an kuma lalata kadarori da dukiyar jama’a tare da banka wa gidajen jama’a wuta a harin da suka kai kauyen Kastina-Ala.

Babban sakataren watsa labaran shugaban karamar hukumar Kastina-Ala, Tertsea Benga, ya shaida cewar zan iya tabbatar da kisan mutum uku ne kawai wadanda aka kai musu hari a gidan tsohon dan majalisar.

Benga ya shaida cewar lamarin ya faru ne cikin daren ranar ta Lahadi.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar DSP Catherine Anene ta tabbatar da mutuwar mutum biyar din, tana mai cewa ba su kai ga kammala tattara bayanan kisan da aka yi a Kastina-Ala ba zuwa yanzu.

Anene ta ce, mutum uku, da ya hada da wani mutum da matarsa da dansa guda ne aka kashe a Kastina-Ala, a kauyen Naka kuma wasu matasa biyu su ma sun rasa rayukansu lamarin da ya kawo adadin mutum biyar wadanda suka mutu.

Ta ce, sun kaddamar da bincike domin kokarin gano musabbabin lamarin tare da yunkurin daukan matakan da suka dace domin dakile faruwar hakan gaba.

SendShareTweetShare
Previous Post

Sanata Lawan Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Sanata Kwankwaso Da Sheikh Lemu

Next Post

Gwamnan Gombe Ya Yi Alhinin Rasuwar Garkuwan Gombe, Sanata Kumo 

RelatedPosts

Abokin Zamansu

Sun Daba Wa Abokin Zamansu Wuka Har Lahira A Legas

by Sulaiman Ibrahim
9 hours ago
0

Wani mutum mai suna Toheeb tare da abokansa a yanzu...

Garkuwa

’Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sanda, Sun Yi Awon Gaba Da Bindigarsa

by Sulaiman Ibrahim
9 hours ago
0

Wasu 'yan bindiga da ba a san ko su wanene...

’Yan Sanda Sun Cafke Wasu Da Ake Zargin ’Yan Kungiyar Asiri Ne A Legas

by Sulaiman Ibrahim
9 hours ago
0

Rundunar ‘yan sanda reshen jihar Legas a jiya, ta ce...

Next Post
Maso Gabas

Gwamnan Gombe Ya Yi Alhinin Rasuwar Garkuwan Gombe, Sanata Kumo 

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version