• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sanda 5 A Imo

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sanda 5 A Imo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan bindiga a safiyar ranar Juma’a sun kashe ‘yan sanda biyar a mahadar Okpala da ke karamar hukumar Ngor Okpala a Jihar Imo.

Haka kuma an kashe wasu ma’aurata masu suna Mista da Misis Chinaka Nwagu wadanda suka fito daga yankin Amankwo Okpala.

  • Sallah: Wamako Ya ‘Yantar Da Fursunoni 62 A Sakkwato
  • Bukatar Magidanta Su Sa Ido Kan Yadda ‘Ya’yansu Za Su Yi Bikin Sallah

Lamarin dai ya jefa daukacin al’ummar yankin cikin firgici saboda ba zato ba tsammani aka kawo karshen harkokin kasuwanci.

Wani dan uwa ga ma’auratan ya shaida wa wakilinmu cewa ‘yan sandan da aka kashe sun taso ne daga sashin ‘yan sanda da ke makwabtaka da Abo Mbaise don cin abinci a mahadar.

Ya ce a yayin da ‘yan sandan ke cin abinci, wasu ‘yan bindiga sun zo wajen inda suka bude musu wuta.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

Ya ce yayin da aka harbe ‘yan sanda uku a wurin, wasu biyu kuma sun gudu zuwa wani waje, amma maharan sun garzaya zuwa shagon da suka fake suka kashe su sannan suka kashe ma’auratan da ke shagon da suka shiga.

Wani ganau ya bayyana cewa bayan kashe ‘yan sandan, ‘yan bindigar sun yi awon gaba da bindigunsu guda biyar.

Majiyar ta ce, “Wannan bakar rana ce a cikin al’ummarmu. Wasu ‘yan bindiga da misalin karfe 8 na safe sun harbe ‘yan sanda biyar har lahira a mahadar Okpala. ‘Yan sandan sun tuka motar Hilux mai launin fari daga sashin ‘yan sanda na Aboh Mbaise don cin abinci a mahadar.

“A lokacin da suke cin abinci, ‘yan bindigar sun dira wajen, suka bude musu wuta. Biyu daga cikin ‘yan sandan biyar sun garzaya zuwa wani shago don fakewa, amma suka bi su suka kashe su tare da wasu ma’aurata.

“Sun kwashe bindigoginsu. Wannan abin takaici ne sosai. Kowa ya rude. Ma’auratan sun yu kaura daga Legas kusan shekara daya da ta wuce. Mun ajiye gawarwakinsu a dakin ajiyar gawa. An rufe kasuwar. Mutane sun gudu sun bar shagunansu.

Wani mai suna Dominic Okpor ya shaida wa wakilinmu cewa ya ga gawarwakin ‘yan sandan da aka kashe a kan hanyar da ya bi ta hanyar Owerri zuwa Aba.

Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Henry Okoye, ya ce har yanzu ba shi da masaniya kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SandaFarmakiHariImoKisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fadar Shugaban Kasa Ta Kare Buhari Kan Ayyukan Da Ya Yi A Mulkinsa

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

13 hours ago
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci
Manyan Labarai

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

18 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

22 hours ago
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
Manyan Labarai

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

23 hours ago
Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar
Manyan Labarai

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

1 day ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

1 day ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.