• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sanda 5 A Imo

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sanda 5 A Imo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘yan bindiga a safiyar ranar Juma’a sun kashe ‘yan sanda biyar a mahadar Okpala da ke karamar hukumar Ngor Okpala a Jihar Imo.

Haka kuma an kashe wasu ma’aurata masu suna Mista da Misis Chinaka Nwagu wadanda suka fito daga yankin Amankwo Okpala.

  • Sallah: Wamako Ya ‘Yantar Da Fursunoni 62 A Sakkwato
  • Bukatar Magidanta Su Sa Ido Kan Yadda ‘Ya’yansu Za Su Yi Bikin Sallah

Lamarin dai ya jefa daukacin al’ummar yankin cikin firgici saboda ba zato ba tsammani aka kawo karshen harkokin kasuwanci.

Wani dan uwa ga ma’auratan ya shaida wa wakilinmu cewa ‘yan sandan da aka kashe sun taso ne daga sashin ‘yan sanda da ke makwabtaka da Abo Mbaise don cin abinci a mahadar.

Ya ce a yayin da ‘yan sandan ke cin abinci, wasu ‘yan bindiga sun zo wajen inda suka bude musu wuta.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Ya ce yayin da aka harbe ‘yan sanda uku a wurin, wasu biyu kuma sun gudu zuwa wani waje, amma maharan sun garzaya zuwa shagon da suka fake suka kashe su sannan suka kashe ma’auratan da ke shagon da suka shiga.

Wani ganau ya bayyana cewa bayan kashe ‘yan sandan, ‘yan bindigar sun yi awon gaba da bindigunsu guda biyar.

Majiyar ta ce, “Wannan bakar rana ce a cikin al’ummarmu. Wasu ‘yan bindiga da misalin karfe 8 na safe sun harbe ‘yan sanda biyar har lahira a mahadar Okpala. ‘Yan sandan sun tuka motar Hilux mai launin fari daga sashin ‘yan sanda na Aboh Mbaise don cin abinci a mahadar.

“A lokacin da suke cin abinci, ‘yan bindigar sun dira wajen, suka bude musu wuta. Biyu daga cikin ‘yan sandan biyar sun garzaya zuwa wani shago don fakewa, amma suka bi su suka kashe su tare da wasu ma’aurata.

“Sun kwashe bindigoginsu. Wannan abin takaici ne sosai. Kowa ya rude. Ma’auratan sun yu kaura daga Legas kusan shekara daya da ta wuce. Mun ajiye gawarwakinsu a dakin ajiyar gawa. An rufe kasuwar. Mutane sun gudu sun bar shagunansu.

Wani mai suna Dominic Okpor ya shaida wa wakilinmu cewa ya ga gawarwakin ‘yan sandan da aka kashe a kan hanyar da ya bi ta hanyar Owerri zuwa Aba.

Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Henry Okoye, ya ce har yanzu ba shi da masaniya kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan SandaFarmakiHariImoKisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Fadar Shugaban Kasa Ta Kare Buhari Kan Ayyukan Da Ya Yi A Mulkinsa

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

9 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

16 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

18 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

19 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

1 day ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.