ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe ‘Yan Sanda 5 A Imo

by Sadiq
3 years ago
Imo

Wasu ‘yan bindiga a safiyar ranar Juma’a sun kashe ‘yan sanda biyar a mahadar Okpala da ke karamar hukumar Ngor Okpala a Jihar Imo.

Haka kuma an kashe wasu ma’aurata masu suna Mista da Misis Chinaka Nwagu wadanda suka fito daga yankin Amankwo Okpala.

  • Sallah: Wamako Ya ‘Yantar Da Fursunoni 62 A Sakkwato
  • Bukatar Magidanta Su Sa Ido Kan Yadda ‘Ya’yansu Za Su Yi Bikin Sallah

Lamarin dai ya jefa daukacin al’ummar yankin cikin firgici saboda ba zato ba tsammani aka kawo karshen harkokin kasuwanci.

ADVERTISEMENT

Wani dan uwa ga ma’auratan ya shaida wa wakilinmu cewa ‘yan sandan da aka kashe sun taso ne daga sashin ‘yan sanda da ke makwabtaka da Abo Mbaise don cin abinci a mahadar.

Ya ce a yayin da ‘yan sandan ke cin abinci, wasu ‘yan bindiga sun zo wajen inda suka bude musu wuta.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

Ya ce yayin da aka harbe ‘yan sanda uku a wurin, wasu biyu kuma sun gudu zuwa wani waje, amma maharan sun garzaya zuwa shagon da suka fake suka kashe su sannan suka kashe ma’auratan da ke shagon da suka shiga.

Wani ganau ya bayyana cewa bayan kashe ‘yan sandan, ‘yan bindigar sun yi awon gaba da bindigunsu guda biyar.

Majiyar ta ce, “Wannan bakar rana ce a cikin al’ummarmu. Wasu ‘yan bindiga da misalin karfe 8 na safe sun harbe ‘yan sanda biyar har lahira a mahadar Okpala. ‘Yan sandan sun tuka motar Hilux mai launin fari daga sashin ‘yan sanda na Aboh Mbaise don cin abinci a mahadar.

“A lokacin da suke cin abinci, ‘yan bindigar sun dira wajen, suka bude musu wuta. Biyu daga cikin ‘yan sandan biyar sun garzaya zuwa wani shago don fakewa, amma suka bi su suka kashe su tare da wasu ma’aurata.

“Sun kwashe bindigoginsu. Wannan abin takaici ne sosai. Kowa ya rude. Ma’auratan sun yu kaura daga Legas kusan shekara daya da ta wuce. Mun ajiye gawarwakinsu a dakin ajiyar gawa. An rufe kasuwar. Mutane sun gudu sun bar shagunansu.

Wani mai suna Dominic Okpor ya shaida wa wakilinmu cewa ya ga gawarwakin ‘yan sandan da aka kashe a kan hanyar da ya bi ta hanyar Owerri zuwa Aba.

Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Henry Okoye, ya ce har yanzu ba shi da masaniya kan lamarin.

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dauki Sabbin Ƴansanda 50,000 Da Karin Sojoji — Tinubu

June 12, 2026
Imo
Manyan Labarai

June 12, 2026
Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya
Manyan Labarai

Takaitaccen Jawabin Shugaban Ƙasa Tinubu Na Ranar Dimokuraɗiyya

June 12, 2026
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.